• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Arsenal

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta shiga tsaka mai wuya bayan da ‘yan wasanta guda biyu, Martin Ordigaard da Ricardo Callafiori suka samu rauni a wasannin da suka bugawa kasashensu na wasannin gasar cin kofin Nations League.

Sannan a wasan kungiyar da Brighton, an ba wa dan wasan Ingila, Declan Rice jan kati, wanda hakan ya sa kungiyar ta tashi wasan 1-1 a filin wasa na Fly Emirates dake birnin landan, kafin a tafi hutun wasannin kasashe. Sannan wani kwamiti mai zaman kansa da ke kula da yanayin alkalanci a gasar Firimiyar Ingila ya ce jan katin da alkalin wasa Chris Kabanagh ya ba wa Rice ya dace kuma kwamitin da yake bitar yadda aka busa wasannin babbar gasar ta Ingila a duk mako, ya ce ya dace da aka kori Rice daga karawar.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Ana Iya Ganin Sabon Karfin Sin A Bikin Baje Kolin CIFTIS

Tun farko an bai wa Rice katin gargadi, sai ya taba kwallo a lokacin da Joel Beltman zai yi bugun tazara a minti na 49 kuma lamarin ya faru ne a wasan Premier League mako na uku da suka tashi 1-1 tsakanin Arsenal da Brighton a Emirates ranar Asabar 31 ga watan Agusta.

Shi ne jan katin farko da aka ba wa Rice a tarihinsa, inda kwamitin ya ce yana sane ya taba kwallon, kenan hukuncin ya dace da shi, wanda tun farko yana da kati mai ruwan dorawa wanda ya samu ana tsaka da fafatawar.

Kwamitin mai zaman kansa ya kunshi tsofaffi uku ko dai ‘yan wasa ko masu horarwa da wakili daga Premier League da wani daga masu alkalancin gasar haka kuma kwamitin ya ce BAR ta yi daidai da hukuncin da ta yanke a kwallon da Trent Aledander-Arnold ya ci a wasan da Liberpool ta ci Manchester United 3-0 a Old Trafford.

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Sai dai kungiyar Arsenal za ta buga wasa biyar cikin Satumba da ya hada da uku a Premier League da Champions League da kuma League Cup inda Tottenham za ta karbi bakuncin Arsenal a wasan hamayya karawar mako na hudu a Premier League ranar 15 ga watan Satumba.

Kuma hakan na zuwa ne a daidai lokacin da dan wasa Martin Ordegaard ya samu rauni a lokacin da yake wakiltar kasarsa ta Norway, sannan shima Ricardo Callafiori ya samu ciwo a lokacin da yake bugawa kasar Italiya wasa da Faransa.

Hakan yana nufin watakila Arsenal za ta buga wasan Tottenham ba tare da ‘yan wasa Ordegaard da Callafiori ba sannan dan wasa Declan Rice ma ba zai buga wasan ba saboda jan katin da aka bashi a wasan Brighton.

Haka kuma Arsenal za ta je Italiya domin karawa da Atalanta a wasan farko a cikin rukuni a Champions League ranar Alhamis 19 ga watan Satumba kuma wannan shi ne karon farko da Atalanta da Arsenal za su kece raini a babbar gasar ta Zakarun Turai a tsakaninsu.

Wasa na uku da Arsenal za ta yi a waje a jere a Satumba, shi ne a gidan Manchester City a mako na biyar a Premier League ranar 22 ga watan Satumba daga nan ne kuma Arsenal za ta karbi bakuncin Bolton a League Cup da za su kece raini a Emirates ranar 25 ga watan Satumba.

Wasa na karshe da Arsenal za ta yi a cikin watan Satumba, shi ne wanda Leicester City za ta je Emirates a mako na shida a babbar gasar ta Ingila ranar 28 ga watan Satumba. Arsenal tana mataki na uku a teburin Premier League da maki bakwai, bayan da ta ci wasa biyu da canjaras daya.

Wasannin da Arsenal za ta kara cikin Satumbar Premier League ranar Lahadi 15 ga watan Satumba

Tottenham da Arsenal Kofin Nahiyar Turai ranar Alhamis 19 ga watan Satumba

Atalanta da Arsenal Kofin Premier ranar Lahadi 22 ga watan Satumba. Man City da Arsenal League Cup ranar Laraba 25 ga watan Satumba Arsenal da Bolton Kofin Premier ranar Asabar 28 ga watan Satumba Arsenal da Leicester.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
Wasanni

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Next Post
Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.