• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

by Abba Ibrahim Wada
8 months ago
in Wasanni
0
Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta shiga tsaka mai wuya bayan da ‘yan wasanta guda biyu, Martin Ordigaard da Ricardo Callafiori suka samu rauni a wasannin da suka bugawa kasashensu na wasannin gasar cin kofin Nations League.

Sannan a wasan kungiyar da Brighton, an ba wa dan wasan Ingila, Declan Rice jan kati, wanda hakan ya sa kungiyar ta tashi wasan 1-1 a filin wasa na Fly Emirates dake birnin landan, kafin a tafi hutun wasannin kasashe. Sannan wani kwamiti mai zaman kansa da ke kula da yanayin alkalanci a gasar Firimiyar Ingila ya ce jan katin da alkalin wasa Chris Kabanagh ya ba wa Rice ya dace kuma kwamitin da yake bitar yadda aka busa wasannin babbar gasar ta Ingila a duk mako, ya ce ya dace da aka kori Rice daga karawar.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Ana Iya Ganin Sabon Karfin Sin A Bikin Baje Kolin CIFTIS

Tun farko an bai wa Rice katin gargadi, sai ya taba kwallo a lokacin da Joel Beltman zai yi bugun tazara a minti na 49 kuma lamarin ya faru ne a wasan Premier League mako na uku da suka tashi 1-1 tsakanin Arsenal da Brighton a Emirates ranar Asabar 31 ga watan Agusta.

Shi ne jan katin farko da aka ba wa Rice a tarihinsa, inda kwamitin ya ce yana sane ya taba kwallon, kenan hukuncin ya dace da shi, wanda tun farko yana da kati mai ruwan dorawa wanda ya samu ana tsaka da fafatawar.

Kwamitin mai zaman kansa ya kunshi tsofaffi uku ko dai ‘yan wasa ko masu horarwa da wakili daga Premier League da wani daga masu alkalancin gasar haka kuma kwamitin ya ce BAR ta yi daidai da hukuncin da ta yanke a kwallon da Trent Aledander-Arnold ya ci a wasan da Liberpool ta ci Manchester United 3-0 a Old Trafford.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Sai dai kungiyar Arsenal za ta buga wasa biyar cikin Satumba da ya hada da uku a Premier League da Champions League da kuma League Cup inda Tottenham za ta karbi bakuncin Arsenal a wasan hamayya karawar mako na hudu a Premier League ranar 15 ga watan Satumba.

Kuma hakan na zuwa ne a daidai lokacin da dan wasa Martin Ordegaard ya samu rauni a lokacin da yake wakiltar kasarsa ta Norway, sannan shima Ricardo Callafiori ya samu ciwo a lokacin da yake bugawa kasar Italiya wasa da Faransa.

Hakan yana nufin watakila Arsenal za ta buga wasan Tottenham ba tare da ‘yan wasa Ordegaard da Callafiori ba sannan dan wasa Declan Rice ma ba zai buga wasan ba saboda jan katin da aka bashi a wasan Brighton.

Haka kuma Arsenal za ta je Italiya domin karawa da Atalanta a wasan farko a cikin rukuni a Champions League ranar Alhamis 19 ga watan Satumba kuma wannan shi ne karon farko da Atalanta da Arsenal za su kece raini a babbar gasar ta Zakarun Turai a tsakaninsu.

Wasa na uku da Arsenal za ta yi a waje a jere a Satumba, shi ne a gidan Manchester City a mako na biyar a Premier League ranar 22 ga watan Satumba daga nan ne kuma Arsenal za ta karbi bakuncin Bolton a League Cup da za su kece raini a Emirates ranar 25 ga watan Satumba.

Wasa na karshe da Arsenal za ta yi a cikin watan Satumba, shi ne wanda Leicester City za ta je Emirates a mako na shida a babbar gasar ta Ingila ranar 28 ga watan Satumba. Arsenal tana mataki na uku a teburin Premier League da maki bakwai, bayan da ta ci wasa biyu da canjaras daya.

Wasannin da Arsenal za ta kara cikin Satumbar Premier League ranar Lahadi 15 ga watan Satumba

Tottenham da Arsenal Kofin Nahiyar Turai ranar Alhamis 19 ga watan Satumba

Atalanta da Arsenal Kofin Premier ranar Lahadi 22 ga watan Satumba. Man City da Arsenal League Cup ranar Laraba 25 ga watan Satumba Arsenal da Bolton Kofin Premier ranar Asabar 28 ga watan Satumba Arsenal da Leicester.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalFirimiyar IngilaGasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

Next Post

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

4 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

4 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

1 week ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.