ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Trump

Tsohon shugaban Amurka kuma dan takarar jamiyyar Republican a zaben kasar mai zuwa Donald Trump da mataimakiyar shugaban kasar kuma ‘yar takarar jamiyyar Democrat, Kamala Harris sun gwabza a kan batun tattalin arziki da ‘yancin zubar da ciki da kuma manufar shige da fice a muhawararsu ta farko a kan zaben shugaban kasar da za a yi a watan Nuwamba.

Muhawarar wadda sau da dama ta kan karkata ga suka da cin dunduniyar juna, ta tabo bangarori da dama da suka kama daga abubuwan da suka jibinci batun manufofi da waje da tattalin arziki.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Muhawarar wadda ta kasance ta farko a tsakaninsu kasancewar ba su taba haduwa gaba da gaba ba ta fara ne da ban mamaki, inda Kamala Harris ta tunkari Donald Trump ta yi musabaha da shi a abin da za a ce musabaha ta farko a wata muhawar ta masu neman shugaban kasa tun 2016.

ADVERTISEMENT

Muhawara dai ta kasance mai muhimmanci musamman ga ita Kamala Harris, wadda kuriar jin ra’ayin jama’a ta nuna cewa sama da kashi daya bisa hudu na masu zabe ke ganin ba su da masaniya sosai a kanta.

‘Yan takarar biyu sun bude muhawara ne da ta hanyar mayar da hankali kan batun tattalin arziki, bangaren da kur’iar jin ra’ayin jama’a ta nuna Trump ya fi dama.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Harris ta soki aniyar Trump ta sanya haraji mai yawa a kan kayayyakin waje, wanda shiri ne da ta kwatanta da haraji a kan masu matsakaicin samu, inda ta tallata shirinta na rage haraji ga iyalai da masu kananan harkokin kasuwanci.

Haka kuma Harris ta soki Trump da janyo rashin akin yi a Amurka a lokacin yana shugaban kasa daga 2017 zuwa 2021.

Sannan shi kuma ya soke ta a kan yawan tashin farashin kaya da ayyuka da ya ce an rika samu a lokacin mulkin Biden, kodayake ya rika kara gishiri a kan yadda aka samu karuwar farashin

Sannan kuma nan da nan ya karkata a kan babban batun da ya fi sanyawa a gaba na shige da fice, inda ya yi ikirari ba tare da wata sheda ba cewa bakin haure sun rika shiga Amurka daga iyakarta ta kudu da Medico.

‘Yar takarar ta Democrat ta gabatar da jawabi mai tsawo na suka a kan ‘yancin zubar da cikin da ake magana kan yadda take ganin an danne wa mata ‘yancinsu na samun kulawar gaggawa a harkar lafiya, da kuma yadda matan suka rasa damar zubar da ciki saboda dokoki na jihohi da suka samu gindin zama tun bayan da kotun kolin kasar ta kawar da damar da jihohi ke da ita a kan hakan a 2022.

Hukuncin da ta danganta da alkalai uku na kotun da Trump ya nada.

A kan manufofin waje Mista Trump ya ki ya masa cewa ko yana ganin ya kamata Ukraine ta yi nasara a yaki da Rasha, yayin da ya zargi Harris da tsanar Isra’ila.

A kan batun na Ukraine Harris tana nuna goyon baya ne ga wadanda ta kira kawayen Amurka, yayin da ta jadda ‘yancin Isra’ila na kare kanta da tabbatar da tsaronta, to amma tana ganin hanyar lafiya ita ce samar da kasashe biyu na Isra’ila da kuma Falasdinawa da ta ce sun cancanci samun tasu kasar cikin ‘yanci da walwala.

Mis Hariis ta soki Trump a kan samun sa da kotu ta yi da laifi a kan shari’arsa ta bayar da kudi na toshiyar baki ga fitaccciyar mai fim din batsa da ya yi mu’amulla da ita da sauran laifuka da aka same shi da su.

Trump ya musanta aikata wani laifi a nan inda ya sake zargin Harris da jam’iyyarta ta Democrat da kulla masa sharri a kan dukkanin wadannan laifuka ba tare da sheda ba.

Haka kuma Trump ya sake ikirarinsa na cewa zaben 2020 ya fadi ne saboda magudi da ya ce an yi masa.

Yanzu dai mako takwas ya rage a yi zaben.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.