ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Trump

Tsohon shugaban Amurka kuma dan takarar jamiyyar Republican a zaben kasar mai zuwa Donald Trump da mataimakiyar shugaban kasar kuma ‘yar takarar jamiyyar Democrat, Kamala Harris sun gwabza a kan batun tattalin arziki da ‘yancin zubar da ciki da kuma manufar shige da fice a muhawararsu ta farko a kan zaben shugaban kasar da za a yi a watan Nuwamba.

Muhawarar wadda sau da dama ta kan karkata ga suka da cin dunduniyar juna, ta tabo bangarori da dama da suka kama daga abubuwan da suka jibinci batun manufofi da waje da tattalin arziki.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Muhawarar wadda ta kasance ta farko a tsakaninsu kasancewar ba su taba haduwa gaba da gaba ba ta fara ne da ban mamaki, inda Kamala Harris ta tunkari Donald Trump ta yi musabaha da shi a abin da za a ce musabaha ta farko a wata muhawar ta masu neman shugaban kasa tun 2016.

ADVERTISEMENT

Muhawara dai ta kasance mai muhimmanci musamman ga ita Kamala Harris, wadda kuriar jin ra’ayin jama’a ta nuna cewa sama da kashi daya bisa hudu na masu zabe ke ganin ba su da masaniya sosai a kanta.

‘Yan takarar biyu sun bude muhawara ne da ta hanyar mayar da hankali kan batun tattalin arziki, bangaren da kur’iar jin ra’ayin jama’a ta nuna Trump ya fi dama.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Harris ta soki aniyar Trump ta sanya haraji mai yawa a kan kayayyakin waje, wanda shiri ne da ta kwatanta da haraji a kan masu matsakaicin samu, inda ta tallata shirinta na rage haraji ga iyalai da masu kananan harkokin kasuwanci.

Haka kuma Harris ta soki Trump da janyo rashin akin yi a Amurka a lokacin yana shugaban kasa daga 2017 zuwa 2021.

Sannan shi kuma ya soke ta a kan yawan tashin farashin kaya da ayyuka da ya ce an rika samu a lokacin mulkin Biden, kodayake ya rika kara gishiri a kan yadda aka samu karuwar farashin

Sannan kuma nan da nan ya karkata a kan babban batun da ya fi sanyawa a gaba na shige da fice, inda ya yi ikirari ba tare da wata sheda ba cewa bakin haure sun rika shiga Amurka daga iyakarta ta kudu da Medico.

‘Yar takarar ta Democrat ta gabatar da jawabi mai tsawo na suka a kan ‘yancin zubar da cikin da ake magana kan yadda take ganin an danne wa mata ‘yancinsu na samun kulawar gaggawa a harkar lafiya, da kuma yadda matan suka rasa damar zubar da ciki saboda dokoki na jihohi da suka samu gindin zama tun bayan da kotun kolin kasar ta kawar da damar da jihohi ke da ita a kan hakan a 2022.

Hukuncin da ta danganta da alkalai uku na kotun da Trump ya nada.

A kan manufofin waje Mista Trump ya ki ya masa cewa ko yana ganin ya kamata Ukraine ta yi nasara a yaki da Rasha, yayin da ya zargi Harris da tsanar Isra’ila.

A kan batun na Ukraine Harris tana nuna goyon baya ne ga wadanda ta kira kawayen Amurka, yayin da ta jadda ‘yancin Isra’ila na kare kanta da tabbatar da tsaronta, to amma tana ganin hanyar lafiya ita ce samar da kasashe biyu na Isra’ila da kuma Falasdinawa da ta ce sun cancanci samun tasu kasar cikin ‘yanci da walwala.

Mis Hariis ta soki Trump a kan samun sa da kotu ta yi da laifi a kan shari’arsa ta bayar da kudi na toshiyar baki ga fitaccciyar mai fim din batsa da ya yi mu’amulla da ita da sauran laifuka da aka same shi da su.

Trump ya musanta aikata wani laifi a nan inda ya sake zargin Harris da jam’iyyarta ta Democrat da kulla masa sharri a kan dukkanin wadannan laifuka ba tare da sheda ba.

Haka kuma Trump ya sake ikirarinsa na cewa zaben 2020 ya fadi ne saboda magudi da ya ce an yi masa.

Yanzu dai mako takwas ya rage a yi zaben.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.