• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Daily Trust Da MacArthur Sun Ba ‘Yan Jarida Horo Kan Bibiyar Kasafin Kudi Da Bincike

by Muhammad
3 years ago
Gidauniyar

A wani bangare na kokarin ba ‘Yan Jarida horo kan dabarun aiki da gogewa a bangaren aikin Jarida, Gidauniyar Daily Trust Foundation masu tashar Trust TV da wallafa Jaridar Daily Trust da Aminiya tare da tallafin Gidauniyar MacArthur sun horar da ‘Yan jarida a Kano.

Horon na kwanaki uku, wanda aka zabo ‘yan jarida kusan 30 daga gidajen jaridu da gidajen rediyo da talabijin daga yankin Arewa maso Yamma, ya ta’allaka ne kan bin diddigin kasafin kudi da kuma binciken yadda ake kashe kudaden al’uma a gwamnatance.

  • Adamu Ya Kori ‘Yan Jarida Daga Ofishin APC Bayan Tutsun Da ‘Yan Jam’iyyar Suka Tayar
  • ‘Yan Sanda A Jihar Osun Sun Bindige ‘Yan Jarida 2 A Lokacin Zanga-zanga

Da yake gabatar da jawabin bude taron, shugaban gidauniyar Daily Trust, Malam Bilya Bala, ya ce horon wani bangare ne na manufofin gidauniyar na kara kwazo ga ‘yan jarida a fadin Nijeriya.

“Abin takaici a cikin ‘yan shekarun nan, mun ci karo da wasu ‘yan jarida da suka bayyana cewa tun bayan kammala karatunsu ba su taba halartar wani horo ba sama da shekaru goma bayan kammala karatun jami’a. Abin ban mamaki ne wannan,”

“Gidauniyar mu a shirye take ta sauya wannan dabi’a, kuma shi ya sa muka tsakulo ‘Yan Jarida daga kafafen yada labarai daban-daban, ba wai Daily Trust kadai ba, domin ku ci gajiyar wannan bita,”

LABARAI MASU NASABA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

“Muna sha’awar horar da ‘yan jarida daga tushe domin aikin jarida a yanzu ya fi na baya fiye da kowane lokaci, a wannan zamani na kafofin watsa labarai na zamani,”

“Binciken kasafin kudi yana da matukar muhimmanci a yunkurinmu na yi wa gwamnati hisabi ga jama’a da kuma mai da hankali kan gaskiya a harkokin mulki a Nijeriya,”

“Ana fitar da kudade mai yawa daga Abuja zuwa jihohi da kananan hukumomi; mataki na biyu da na uku na gwamnati na karbar haraji da kudaden shiga daban-daban, wanda ba kasafai suke kashe wa jama’a ba.”

A nasa bangaren, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba, wanda Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Inuwa Yakasai ya wakilta, ya gode wa wadanda suka shirya wannan taro da ya bayyana a matsayin taron ga jama’a masu kishin kasa wadanda a kodayaushe suke tabbatar da cewa an samu nagartaccen aiki.

Ya ba da tabbacin gwamnatin jihar Kano a shirye ta ke ta ci gaba da bayar da hadin kai da bayar da kwarin guiwa a wannan fanni.

Wadanda suka jagoranci horon sun hada da tsohon kwamishinan kudi na jihar Kano, Farfesa Kabir Isah Dandago da Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Theophilus Abbah da kuma Caheles Mba daga kamfanin Dataphyte da Atiku Samuel da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Next Post
Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.