• Leadership Hausa
Friday, August 19, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Gidauniyar Daily Trust Da MacArthur Sun Ba ‘Yan Jarida Horo Kan Bibiyar Kasafin Kudi Da Bincike

by Muhammad
2 months ago
in Labarai
0
Gidauniyar Daily Trust Da MacArthur Sun Ba ‘Yan Jarida Horo Kan Bibiyar Kasafin Kudi Da Bincike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani bangare na kokarin ba ‘Yan Jarida horo kan dabarun aiki da gogewa a bangaren aikin Jarida, Gidauniyar Daily Trust Foundation masu tashar Trust TV da wallafa Jaridar Daily Trust da Aminiya tare da tallafin Gidauniyar MacArthur sun horar da ‘Yan jarida a Kano.

Horon na kwanaki uku, wanda aka zabo ‘yan jarida kusan 30 daga gidajen jaridu da gidajen rediyo da talabijin daga yankin Arewa maso Yamma, ya ta’allaka ne kan bin diddigin kasafin kudi da kuma binciken yadda ake kashe kudaden al’uma a gwamnatance.

  • Adamu Ya Kori ‘Yan Jarida Daga Ofishin APC Bayan Tutsun Da ‘Yan Jam’iyyar Suka Tayar
  • ‘Yan Sanda A Jihar Osun Sun Bindige ‘Yan Jarida 2 A Lokacin Zanga-zanga

Da yake gabatar da jawabin bude taron, shugaban gidauniyar Daily Trust, Malam Bilya Bala, ya ce horon wani bangare ne na manufofin gidauniyar na kara kwazo ga ‘yan jarida a fadin Nijeriya.

“Abin takaici a cikin ‘yan shekarun nan, mun ci karo da wasu ‘yan jarida da suka bayyana cewa tun bayan kammala karatunsu ba su taba halartar wani horo ba sama da shekaru goma bayan kammala karatun jami’a. Abin ban mamaki ne wannan,”

“Gidauniyar mu a shirye take ta sauya wannan dabi’a, kuma shi ya sa muka tsakulo ‘Yan Jarida daga kafafen yada labarai daban-daban, ba wai Daily Trust kadai ba, domin ku ci gajiyar wannan bita,”

Labarai Masu Nasaba

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

“Muna sha’awar horar da ‘yan jarida daga tushe domin aikin jarida a yanzu ya fi na baya fiye da kowane lokaci, a wannan zamani na kafofin watsa labarai na zamani,”

“Binciken kasafin kudi yana da matukar muhimmanci a yunkurinmu na yi wa gwamnati hisabi ga jama’a da kuma mai da hankali kan gaskiya a harkokin mulki a Nijeriya,”

“Ana fitar da kudade mai yawa daga Abuja zuwa jihohi da kananan hukumomi; mataki na biyu da na uku na gwamnati na karbar haraji da kudaden shiga daban-daban, wanda ba kasafai suke kashe wa jama’a ba.”

A nasa bangaren, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba, wanda Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Inuwa Yakasai ya wakilta, ya gode wa wadanda suka shirya wannan taro da ya bayyana a matsayin taron ga jama’a masu kishin kasa wadanda a kodayaushe suke tabbatar da cewa an samu nagartaccen aiki.

Ya ba da tabbacin gwamnatin jihar Kano a shirye ta ke ta ci gaba da bayar da hadin kai da bayar da kwarin guiwa a wannan fanni.

Wadanda suka jagoranci horon sun hada da tsohon kwamishinan kudi na jihar Kano, Farfesa Kabir Isah Dandago da Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Theophilus Abbah da kuma Caheles Mba daga kamfanin Dataphyte da Atiku Samuel da dai sauransu.

Tags: 'Yan JaridaDaily TrustHoroJaridakanoMacArthur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Ware Sojoji 5,800 Domin Tunkarar Yaki Da ‘Yan Ta’adda —Shugaban Soji

Next Post

Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

Related

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara
Rahotonni

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

39 mins ago
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa
Labarai

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

39 mins ago
Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa
Kananan Labarai

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

1 hour ago
srilanka
Rahotonni

Darussa Daga Gwagwarmayar Kasar Sri Lanka (Nazari)

3 hours ago
Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki
Labarai

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

4 hours ago
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu
Labarai

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

5 hours ago
Next Post
Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

August 19, 2022
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

August 19, 2022
Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

August 19, 2022
Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

August 19, 2022
Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

August 19, 2022
srilanka

Darussa Daga Gwagwarmayar Kasar Sri Lanka (Nazari)

August 19, 2022
Goro

Goron Jumu’a

August 19, 2022
Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

August 19, 2022
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

August 19, 2022
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

August 19, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.