ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Daily Trust Da MacArthur Sun Ba ‘Yan Jarida Horo Kan Bibiyar Kasafin Kudi Da Bincike

by Muhammad
4 years ago
Gidauniyar

A wani bangare na kokarin ba ‘Yan Jarida horo kan dabarun aiki da gogewa a bangaren aikin Jarida, Gidauniyar Daily Trust Foundation masu tashar Trust TV da wallafa Jaridar Daily Trust da Aminiya tare da tallafin Gidauniyar MacArthur sun horar da ‘Yan jarida a Kano.

Horon na kwanaki uku, wanda aka zabo ‘yan jarida kusan 30 daga gidajen jaridu da gidajen rediyo da talabijin daga yankin Arewa maso Yamma, ya ta’allaka ne kan bin diddigin kasafin kudi da kuma binciken yadda ake kashe kudaden al’uma a gwamnatance.

  • Adamu Ya Kori ‘Yan Jarida Daga Ofishin APC Bayan Tutsun Da ‘Yan Jam’iyyar Suka Tayar
  • ‘Yan Sanda A Jihar Osun Sun Bindige ‘Yan Jarida 2 A Lokacin Zanga-zanga

Da yake gabatar da jawabin bude taron, shugaban gidauniyar Daily Trust, Malam Bilya Bala, ya ce horon wani bangare ne na manufofin gidauniyar na kara kwazo ga ‘yan jarida a fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Abin takaici a cikin ‘yan shekarun nan, mun ci karo da wasu ‘yan jarida da suka bayyana cewa tun bayan kammala karatunsu ba su taba halartar wani horo ba sama da shekaru goma bayan kammala karatun jami’a. Abin ban mamaki ne wannan,”

“Gidauniyar mu a shirye take ta sauya wannan dabi’a, kuma shi ya sa muka tsakulo ‘Yan Jarida daga kafafen yada labarai daban-daban, ba wai Daily Trust kadai ba, domin ku ci gajiyar wannan bita,”

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

“Muna sha’awar horar da ‘yan jarida daga tushe domin aikin jarida a yanzu ya fi na baya fiye da kowane lokaci, a wannan zamani na kafofin watsa labarai na zamani,”

“Binciken kasafin kudi yana da matukar muhimmanci a yunkurinmu na yi wa gwamnati hisabi ga jama’a da kuma mai da hankali kan gaskiya a harkokin mulki a Nijeriya,”

“Ana fitar da kudade mai yawa daga Abuja zuwa jihohi da kananan hukumomi; mataki na biyu da na uku na gwamnati na karbar haraji da kudaden shiga daban-daban, wanda ba kasafai suke kashe wa jama’a ba.”

A nasa bangaren, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba, wanda Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Inuwa Yakasai ya wakilta, ya gode wa wadanda suka shirya wannan taro da ya bayyana a matsayin taron ga jama’a masu kishin kasa wadanda a kodayaushe suke tabbatar da cewa an samu nagartaccen aiki.

Ya ba da tabbacin gwamnatin jihar Kano a shirye ta ke ta ci gaba da bayar da hadin kai da bayar da kwarin guiwa a wannan fanni.

Wadanda suka jagoranci horon sun hada da tsohon kwamishinan kudi na jihar Kano, Farfesa Kabir Isah Dandago da Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Theophilus Abbah da kuma Caheles Mba daga kamfanin Dataphyte da Atiku Samuel da dai sauransu.

Gidauniyar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.