ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Daily Trust Da MacArthur Sun Ba ‘Yan Jarida Horo Kan Bibiyar Kasafin Kudi Da Bincike

by Muhammad
4 years ago
Gidauniyar

A wani bangare na kokarin ba ‘Yan Jarida horo kan dabarun aiki da gogewa a bangaren aikin Jarida, Gidauniyar Daily Trust Foundation masu tashar Trust TV da wallafa Jaridar Daily Trust da Aminiya tare da tallafin Gidauniyar MacArthur sun horar da ‘Yan jarida a Kano.

Horon na kwanaki uku, wanda aka zabo ‘yan jarida kusan 30 daga gidajen jaridu da gidajen rediyo da talabijin daga yankin Arewa maso Yamma, ya ta’allaka ne kan bin diddigin kasafin kudi da kuma binciken yadda ake kashe kudaden al’uma a gwamnatance.

  • Adamu Ya Kori ‘Yan Jarida Daga Ofishin APC Bayan Tutsun Da ‘Yan Jam’iyyar Suka Tayar
  • ‘Yan Sanda A Jihar Osun Sun Bindige ‘Yan Jarida 2 A Lokacin Zanga-zanga

Da yake gabatar da jawabin bude taron, shugaban gidauniyar Daily Trust, Malam Bilya Bala, ya ce horon wani bangare ne na manufofin gidauniyar na kara kwazo ga ‘yan jarida a fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Abin takaici a cikin ‘yan shekarun nan, mun ci karo da wasu ‘yan jarida da suka bayyana cewa tun bayan kammala karatunsu ba su taba halartar wani horo ba sama da shekaru goma bayan kammala karatun jami’a. Abin ban mamaki ne wannan,”

“Gidauniyar mu a shirye take ta sauya wannan dabi’a, kuma shi ya sa muka tsakulo ‘Yan Jarida daga kafafen yada labarai daban-daban, ba wai Daily Trust kadai ba, domin ku ci gajiyar wannan bita,”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Muna sha’awar horar da ‘yan jarida daga tushe domin aikin jarida a yanzu ya fi na baya fiye da kowane lokaci, a wannan zamani na kafofin watsa labarai na zamani,”

“Binciken kasafin kudi yana da matukar muhimmanci a yunkurinmu na yi wa gwamnati hisabi ga jama’a da kuma mai da hankali kan gaskiya a harkokin mulki a Nijeriya,”

“Ana fitar da kudade mai yawa daga Abuja zuwa jihohi da kananan hukumomi; mataki na biyu da na uku na gwamnati na karbar haraji da kudaden shiga daban-daban, wanda ba kasafai suke kashe wa jama’a ba.”

A nasa bangaren, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba, wanda Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Inuwa Yakasai ya wakilta, ya gode wa wadanda suka shirya wannan taro da ya bayyana a matsayin taron ga jama’a masu kishin kasa wadanda a kodayaushe suke tabbatar da cewa an samu nagartaccen aiki.

Ya ba da tabbacin gwamnatin jihar Kano a shirye ta ke ta ci gaba da bayar da hadin kai da bayar da kwarin guiwa a wannan fanni.

Wadanda suka jagoranci horon sun hada da tsohon kwamishinan kudi na jihar Kano, Farfesa Kabir Isah Dandago da Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Theophilus Abbah da kuma Caheles Mba daga kamfanin Dataphyte da Atiku Samuel da dai sauransu.

Gidauniyar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

Ministan Tsaron Sin Ya Yi Magana Kan Hangen Nesan Kasar Sin Game Da Tsarin Yanki A Taron Tattaunawa Na Shangri-La Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.