• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
Sheikh Dahiru Bauchi

Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi ta tura ɗalibai 117 ƙasar Algeria domin yin karatu a ɓangarori daban-daban ciki har da ilimin likitanci, injiniyanci da sauran muhimman ɓangarori na ilimi.

 

Daraktan sashin ilimi na gidauniyar, Gwani Aliyu Dahiru Bauchi, ya yi bayanin cewa dukkanin ɗaliban da suka samu guraben karatun su 140 ne, inda a yanzu haka 117 suka kammala shirin su na tafiya yayin da sauran 23 kuma za su tafi daga baya bayan kammala cike sauran ƙa’idoji.

  • Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo
  • Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Ya ce ɗaliban sun fito ne daga jihohi sama da bakwai da suka haɗa da Bauchi, Gombe, Yobe, Kaduna, Taraba, Adamawa da sauran jihohin da suke Nijeriya.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Sayyidi Aliyu ya shaida hakan ne yayin jawabin bankwana da wayar da kan ɗaliban da suka samu gurbin karatun zuwa ƙasar Algeria na shekarar 2025, da ya gudana a cibiyar Sheikh Dahiru da ke Bauchi a ranar Litinin 13 ga watan Oktoba.

 

Ya ce an ɗauki tsawon lokaci ana wayar da kan ɗaliban na tsawon shekara guda kan yadda za su kyautata rayuwarsu a can ƙasar da kuma samun ilimin da ake tsammani a garesu ba tare da matsaloli ba tare da koyar musu harsunan Farsanci da Larabci domin sauƙaƙa musu fara rayuwa a ƙasar Algeria.

 

Ya yaba wa Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad bisa biyan kuɗin jirgi wa dukkani ɗaliban jihar su 50 daga cikin waɗanda za su tafi ƙasar neman ilimi.

 

Kazalika, ya kuma gode wa gwamnan bisa roƙa musu da ya yi na cewar a bai wa ‘yan Nijeriya damar koyon ilimin likitanci, “A lokacin da tawaga daga Algeriya suka zo jihar Bauchi, gwamna Bala Muhammad ya yi roƙo na cewar a ake amincewa ɗaliban Nijeriya samun ilimin likitanci a ƙasar Algeriya, wanda a da baya ba su bai wa kowa damar samun wannan sai ‘yan ƙasar amma suka amince, lallai wannan abun yabo ne sosai,” ya shaida.

 

Ya ce bayan kuɗin ticket komai na hidimar karatun kyauta ne wanda gwamnatin ƙasar Algeria ta ɗauki nauyi ga waɗanda suka samu nasarar samun guraben, wanda suke da damar yin karatu daga digiri har digiri na biyu (masters), sai ya yi bayanin cewa suna kan ƙoƙarin neman damar samar wa ɗalibai guraren digirin digirgir (PhD).

 

Ya ƙara da cewa wannan shi ne karo na biyu domin a farko gidauniya ta tura ɗalibai 66 zuwa ƙasar Algeriya wanda zuwa yanzu wasu ma har sun kammala digiri a fannonin ilimi daban-daban.

 

Jagoran ya nuna kwarin guiwar cewa idan ɗaliban suka kammala karatun nasu, ƙasar Nijeriya za ta moresu matuƙa gaya. Ya hori ɗaliban da suka samu tallafin karatun da su maida hankali wajen yin abun da ya kamata domin samun ilimi mai inganci tare da nemansu da su zama jakadu na kwarai ga Nigeria.

 

Kazalika, ya jinjina wa Sheikh Dahiru Usman Bauchi bisa gayar gudunmawar da yake bayarwa wajen kyautata harkokin ilimin addini da na zamani, ya ce, bayan gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da mahaddata yanzu haka ana samun masu karatu a ɓangarori daban-daban na ilimi sakamakon ƙoƙarinsa.

 

Sadiyya Auwal wacce ta samu gurbin karatu domin karanta ilimin likitanci, ta gode wa Sheikh Dahiru da daraktan ilimin gidauniyar bisa kokarinsu da ya kai su ga samun damar karatun tare da tabbatar da cewa za ta maida hankali domin samun nasarar abun da za ta je yi can ƙasar Algeria.

 

Shi ma Mukhtar Ahmed wanda ya samu gurbin ƙaratun ilimin kimiyyar na’ura mai ƙwaƙwalwa (Computer Science) ya nuna godiya wa gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi kan damar da ta samar musu, ya ce tsawon shekara ana faɗi tashi don nema musu tafiya karatun.

 

Ya bada tabbacin maida hankali domin samun ilimi mai inganci tare da dawowa Nijeriya domin bayar da nasa gudunmawar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.