• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya nuna matuka farin cikinsa bisa yadda ya ce ya gano Jihar Gombe tana kan turbar kawo sauyi a harkar kasuwanci wanda hakan ya kai ga kasancewar ta a matsayin wacce ta yi fintinkau kan sauran jihohi a bangaren saukaka harkokin gudanar da kasuwanci.

Mataimain shugaban kasan wanda ke wannan jawabin a wajen bikin rufe taron zuba jari na Jihar Gombe da ya gudana a makon jiya, ya ce kamar yadda rahoton kwamitin fadar shugaban kasa kan harkokin kasuwanci ya bayyana cewa jihar ita ce jagaba a fannin tsari da kuma saukaka sana’o’i da harkokin kwadago.

  • Jihar Gombe Ta Samu Nasarori Cikin Shekaru 26 Da Kafuwarta – Gwamna Inuwa 

Ya ce taron zuba jari irin sa na farko ya dace da kudurin Jihar Gombe na samar da kyakkywan yanayin kai wa ga ci gaba mai dorewa, karuwar arziki, zaman lafiya, hadin kai da ci gaba ga al’ummar jihar, kamar yadda yake kunshe a cikin kundin ci gaba na Jihar Gombe na shekaru goma daga 2021 zuwa 2030.

“Wannan kundin ci gaba, yana daya daga cikin na gaba-gaba da wata jiha ta samar, wadda ya yi cikakken bayani kan kudurori da tsare-tsaren jihar na dogon zango don nausa ta gaba. Baya ga wannan, Gombe ta samar da cikakken tsarin kashe kudade na matsakaicin zango daga 2020 zuwa 2022.”
Yemi Osinbajo ya kara da cewa, “Idan za ku iya tunawa, watanni 18 da suka gabata, na zo nan Gombe don bikin baje kolin kayayyakin da masana’antu karo na 27, inda na ziyarci cibiyoyin matsar mai da sarrafa shinkafa, kuma na ga daruruwan buhunan shinkafa da ake sarrafawa a duk rana.

“To yanzu dai za mu iya bugun kirjin cewa Gombe ta dauki aniyar nausa burin ta na zuba jari zuwa mataki na gaba ta hanyar shirya wannan muhimmin taro. Harkokin kasuwanci na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasarmu.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Wannan ya kara zama abu mai muhimmanci ganin yadda muke da dimbin damammaki musamman ganin yadda aka sanya hannu kan yarjejeniyar harkokin kasuwanci maras ka’idi ta Afirka (AfCFTA).

Mataimakin shugaban kasan ya yi kira ga sauran jihohi da su yi koyi da Jihar Gombe, domin tattalin arzikin kasar nan ya samu hababa, kana ya bayyana godiyarsa ga kamfanonin da suke zuba jari na ciki da waje tare da kiransu da su kara hakan domin ci gaban Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Anambra Ta Bayar Da Umarnin Garkame Gidajen Caca

Next Post

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

1 hour ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

3 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

3 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

4 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

7 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

9 hours ago
Next Post
A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.