• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya nuna matuka farin cikinsa bisa yadda ya ce ya gano Jihar Gombe tana kan turbar kawo sauyi a harkar kasuwanci wanda hakan ya kai ga kasancewar ta a matsayin wacce ta yi fintinkau kan sauran jihohi a bangaren saukaka harkokin gudanar da kasuwanci.

Mataimain shugaban kasan wanda ke wannan jawabin a wajen bikin rufe taron zuba jari na Jihar Gombe da ya gudana a makon jiya, ya ce kamar yadda rahoton kwamitin fadar shugaban kasa kan harkokin kasuwanci ya bayyana cewa jihar ita ce jagaba a fannin tsari da kuma saukaka sana’o’i da harkokin kwadago.

  • Jihar Gombe Ta Samu Nasarori Cikin Shekaru 26 Da Kafuwarta – Gwamna Inuwa 

Ya ce taron zuba jari irin sa na farko ya dace da kudurin Jihar Gombe na samar da kyakkywan yanayin kai wa ga ci gaba mai dorewa, karuwar arziki, zaman lafiya, hadin kai da ci gaba ga al’ummar jihar, kamar yadda yake kunshe a cikin kundin ci gaba na Jihar Gombe na shekaru goma daga 2021 zuwa 2030.

“Wannan kundin ci gaba, yana daya daga cikin na gaba-gaba da wata jiha ta samar, wadda ya yi cikakken bayani kan kudurori da tsare-tsaren jihar na dogon zango don nausa ta gaba. Baya ga wannan, Gombe ta samar da cikakken tsarin kashe kudade na matsakaicin zango daga 2020 zuwa 2022.”
Yemi Osinbajo ya kara da cewa, “Idan za ku iya tunawa, watanni 18 da suka gabata, na zo nan Gombe don bikin baje kolin kayayyakin da masana’antu karo na 27, inda na ziyarci cibiyoyin matsar mai da sarrafa shinkafa, kuma na ga daruruwan buhunan shinkafa da ake sarrafawa a duk rana.

“To yanzu dai za mu iya bugun kirjin cewa Gombe ta dauki aniyar nausa burin ta na zuba jari zuwa mataki na gaba ta hanyar shirya wannan muhimmin taro. Harkokin kasuwanci na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasarmu.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Wannan ya kara zama abu mai muhimmanci ganin yadda muke da dimbin damammaki musamman ganin yadda aka sanya hannu kan yarjejeniyar harkokin kasuwanci maras ka’idi ta Afirka (AfCFTA).

Mataimakin shugaban kasan ya yi kira ga sauran jihohi da su yi koyi da Jihar Gombe, domin tattalin arzikin kasar nan ya samu hababa, kana ya bayyana godiyarsa ga kamfanonin da suke zuba jari na ciki da waje tare da kiransu da su kara hakan domin ci gaban Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Anambra Ta Bayar Da Umarnin Garkame Gidajen Caca

Next Post

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

43 minutes ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

47 minutes ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

49 minutes ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 hour ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

2 hours ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

3 hours ago
Next Post
A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.