ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gombe

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya nuna matuka farin cikinsa bisa yadda ya ce ya gano Jihar Gombe tana kan turbar kawo sauyi a harkar kasuwanci wanda hakan ya kai ga kasancewar ta a matsayin wacce ta yi fintinkau kan sauran jihohi a bangaren saukaka harkokin gudanar da kasuwanci.

Mataimain shugaban kasan wanda ke wannan jawabin a wajen bikin rufe taron zuba jari na Jihar Gombe da ya gudana a makon jiya, ya ce kamar yadda rahoton kwamitin fadar shugaban kasa kan harkokin kasuwanci ya bayyana cewa jihar ita ce jagaba a fannin tsari da kuma saukaka sana’o’i da harkokin kwadago.

  • Jihar Gombe Ta Samu Nasarori Cikin Shekaru 26 Da Kafuwarta – Gwamna Inuwa 

Ya ce taron zuba jari irin sa na farko ya dace da kudurin Jihar Gombe na samar da kyakkywan yanayin kai wa ga ci gaba mai dorewa, karuwar arziki, zaman lafiya, hadin kai da ci gaba ga al’ummar jihar, kamar yadda yake kunshe a cikin kundin ci gaba na Jihar Gombe na shekaru goma daga 2021 zuwa 2030.

ADVERTISEMENT

“Wannan kundin ci gaba, yana daya daga cikin na gaba-gaba da wata jiha ta samar, wadda ya yi cikakken bayani kan kudurori da tsare-tsaren jihar na dogon zango don nausa ta gaba. Baya ga wannan, Gombe ta samar da cikakken tsarin kashe kudade na matsakaicin zango daga 2020 zuwa 2022.”
Yemi Osinbajo ya kara da cewa, “Idan za ku iya tunawa, watanni 18 da suka gabata, na zo nan Gombe don bikin baje kolin kayayyakin da masana’antu karo na 27, inda na ziyarci cibiyoyin matsar mai da sarrafa shinkafa, kuma na ga daruruwan buhunan shinkafa da ake sarrafawa a duk rana.

“To yanzu dai za mu iya bugun kirjin cewa Gombe ta dauki aniyar nausa burin ta na zuba jari zuwa mataki na gaba ta hanyar shirya wannan muhimmin taro. Harkokin kasuwanci na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasarmu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Wannan ya kara zama abu mai muhimmanci ganin yadda muke da dimbin damammaki musamman ganin yadda aka sanya hannu kan yarjejeniyar harkokin kasuwanci maras ka’idi ta Afirka (AfCFTA).

Mataimakin shugaban kasan ya yi kira ga sauran jihohi da su yi koyi da Jihar Gombe, domin tattalin arzikin kasar nan ya samu hababa, kana ya bayyana godiyarsa ga kamfanonin da suke zuba jari na ciki da waje tare da kiransu da su kara hakan domin ci gaban Nijeriya.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.