ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Na Daga Cikin Jihohin Da Ake Fatan Bunkasar Harkokin Kasuwanci – Osinbajo

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gombe

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya nuna matuka farin cikinsa bisa yadda ya ce ya gano Jihar Gombe tana kan turbar kawo sauyi a harkar kasuwanci wanda hakan ya kai ga kasancewar ta a matsayin wacce ta yi fintinkau kan sauran jihohi a bangaren saukaka harkokin gudanar da kasuwanci.

Mataimain shugaban kasan wanda ke wannan jawabin a wajen bikin rufe taron zuba jari na Jihar Gombe da ya gudana a makon jiya, ya ce kamar yadda rahoton kwamitin fadar shugaban kasa kan harkokin kasuwanci ya bayyana cewa jihar ita ce jagaba a fannin tsari da kuma saukaka sana’o’i da harkokin kwadago.

  • Jihar Gombe Ta Samu Nasarori Cikin Shekaru 26 Da Kafuwarta – Gwamna Inuwa 

Ya ce taron zuba jari irin sa na farko ya dace da kudurin Jihar Gombe na samar da kyakkywan yanayin kai wa ga ci gaba mai dorewa, karuwar arziki, zaman lafiya, hadin kai da ci gaba ga al’ummar jihar, kamar yadda yake kunshe a cikin kundin ci gaba na Jihar Gombe na shekaru goma daga 2021 zuwa 2030.

ADVERTISEMENT

“Wannan kundin ci gaba, yana daya daga cikin na gaba-gaba da wata jiha ta samar, wadda ya yi cikakken bayani kan kudurori da tsare-tsaren jihar na dogon zango don nausa ta gaba. Baya ga wannan, Gombe ta samar da cikakken tsarin kashe kudade na matsakaicin zango daga 2020 zuwa 2022.”
Yemi Osinbajo ya kara da cewa, “Idan za ku iya tunawa, watanni 18 da suka gabata, na zo nan Gombe don bikin baje kolin kayayyakin da masana’antu karo na 27, inda na ziyarci cibiyoyin matsar mai da sarrafa shinkafa, kuma na ga daruruwan buhunan shinkafa da ake sarrafawa a duk rana.

“To yanzu dai za mu iya bugun kirjin cewa Gombe ta dauki aniyar nausa burin ta na zuba jari zuwa mataki na gaba ta hanyar shirya wannan muhimmin taro. Harkokin kasuwanci na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasarmu.

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

Wannan ya kara zama abu mai muhimmanci ganin yadda muke da dimbin damammaki musamman ganin yadda aka sanya hannu kan yarjejeniyar harkokin kasuwanci maras ka’idi ta Afirka (AfCFTA).

Mataimakin shugaban kasan ya yi kira ga sauran jihohi da su yi koyi da Jihar Gombe, domin tattalin arzikin kasar nan ya samu hababa, kana ya bayyana godiyarsa ga kamfanonin da suke zuba jari na ciki da waje tare da kiransu da su kara hakan domin ci gaban Nijeriya.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Labarai

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.