ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

by Sulaiman
6 days ago
Dauda lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama wani muhimmin tarihi a tafiyar shugabancinsa.

A ranar Litinin ne gwamnan ya jagoranci wannan zama na 58 a zauren majalisar da ke Fadar Gwamnati a Gusau, inda aka tattauna manyan batutuwan ci gaban jihar tare da yanke muhimman shawarwari da amincewa da ayyukan da suka shafi jin daɗin al’ummar Zamfara.

  • Trump Na Murna Sosai Da Samar Da Matatar Manmu – Dangote
  • Har Yanzu Ana Yi Wa Matatar Man Mu Bita Da Ƙulli – Dangote

Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa a shekarar 2025 kaɗai, Gwamna Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwa guda 23, lamarin da ke nuna irin ƙarfin kulawa da jagoranci da yake bai wa harkokin mulki.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, tun bayan rantsar da shi a watan Mayun 2023, Gwamna Lawal ya kasance kan gaba wajen jagorantar majalisar, inda ya jagoranci zaman 13 a shekarar 2023, sannan 22 a shekarar 2024, kafin a kai ga 23 a shekarar nan ta 2025. Wannan ya kai adadin zaman da ya jagoranta zuwa 58 baki ɗaya.

Sanarwar ta ce, a waɗannan zaman majalisar, ana tattauna muhimman manufofi da tsare-tsaren gwamnati, ciki har da Shirin Ci Gaban Jihar na Shekaru Goma, tare da amincewa da ayyukan raya ƙasa da dama da ke shafar fannoni irin su ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, tattalin arziki da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Gwamnatin ta ƙara da cewa, yawancin ayyukan da majalisar ta amince da su sun kammala ko kuma suna kan hanyar kammalawa.

Daga cikin manyan ayyukan da aka ambata akwai Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa, wanda ke daf da kammaluwa, da kuma gyare-gyare da sabunta kayan aiki a asibitocin gwamnati a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

Haka kuma, an ambaci gini, gyarawa da samar da kayan aiki ga makarantu sama da 500 a faɗin jihar, tare da gina hanyoyin cikin gari a Gusau da sauran ƙananan hukumomi.

Gwamnatin ta ce, waɗannan ayyuka sun haifar da gagarumin canji da ci gaba da jama’a ke gani a sassa daban-daban na jihar.

Da wannan zama na 58, gwamnatin ta bayyana cewa Gwamna Dauda Lawal ya bambanta kansa a cikin takwarorin sa, inda ya zama gwamnan da ya fi kowa jagorantar zaman majalisar zartarwa a cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Next Post
Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.