ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

by Sulaiman
9 months ago
Dauda lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama wani muhimmin tarihi a tafiyar shugabancinsa.

A ranar Litinin ne gwamnan ya jagoranci wannan zama na 58 a zauren majalisar da ke Fadar Gwamnati a Gusau, inda aka tattauna manyan batutuwan ci gaban jihar tare da yanke muhimman shawarwari da amincewa da ayyukan da suka shafi jin daɗin al’ummar Zamfara.

  • Trump Na Murna Sosai Da Samar Da Matatar Manmu – Dangote
  • Har Yanzu Ana Yi Wa Matatar Man Mu Bita Da Ƙulli – Dangote

Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa a shekarar 2025 kaɗai, Gwamna Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwa guda 23, lamarin da ke nuna irin ƙarfin kulawa da jagoranci da yake bai wa harkokin mulki.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, tun bayan rantsar da shi a watan Mayun 2023, Gwamna Lawal ya kasance kan gaba wajen jagorantar majalisar, inda ya jagoranci zaman 13 a shekarar 2023, sannan 22 a shekarar 2024, kafin a kai ga 23 a shekarar nan ta 2025. Wannan ya kai adadin zaman da ya jagoranta zuwa 58 baki ɗaya.

Sanarwar ta ce, a waɗannan zaman majalisar, ana tattauna muhimman manufofi da tsare-tsaren gwamnati, ciki har da Shirin Ci Gaban Jihar na Shekaru Goma, tare da amincewa da ayyukan raya ƙasa da dama da ke shafar fannoni irin su ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, tattalin arziki da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Gwamnatin ta ƙara da cewa, yawancin ayyukan da majalisar ta amince da su sun kammala ko kuma suna kan hanyar kammalawa.

Daga cikin manyan ayyukan da aka ambata akwai Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa, wanda ke daf da kammaluwa, da kuma gyare-gyare da sabunta kayan aiki a asibitocin gwamnati a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

Haka kuma, an ambaci gini, gyarawa da samar da kayan aiki ga makarantu sama da 500 a faɗin jihar, tare da gina hanyoyin cikin gari a Gusau da sauran ƙananan hukumomi.

Gwamnatin ta ce, waɗannan ayyuka sun haifar da gagarumin canji da ci gaba da jama’a ke gani a sassa daban-daban na jihar.

Da wannan zama na 58, gwamnatin ta bayyana cewa Gwamna Dauda Lawal ya bambanta kansa a cikin takwarorin sa, inda ya zama gwamnan da ya fi kowa jagorantar zaman majalisar zartarwa a cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata.

Dauda lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Dauda lawal
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Next Post
Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

LABARAI MASU NASABA

Dauda lawal

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.