• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

A jiya Alhamis ne Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya karɓi baƙuncin matar nan da ‘yan bindiga suka raba da muhallinta da aka yaɗa a wani faifan bidiyo.
Faiaifan bidiyon ya nuna wata uwa da ‘ya’yanta tana bayani a kan ‘yan bindiga suka tilasta musu cin ciyawa domin su tsira da rayukansu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar ta Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce halin da matar wacce ta rasa matsugunin ke ciki ya nuna cewa akwai bukatar a ɗauki matakin gaggawa don magance musabbabin Ibtila’in da yake raba mutane da muhallansu same su da kuma samar matakawuna da kuma tabbatar da cewa iyalai suna samun abubuwan bukata na rayuwa.

  • Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso
  • NIS Ta Samar Da Fasfo 204,332 Cikin Mako Uku – Adepoju

Ta ƙara da cewa Gwamnan ya karɓi baƙuncin matar da ta rasa muhallin nata ne a matsayin nuni kan jajircewarsa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara.

gwamna
“A yau (Alhamis) ne Gwamna Dauda Lawal ya karbi baƙuncin Hauwa’u Halliru, wadda ta rasa komi a dalilin tu’annatin ‘yan fashin daji.
“Gwamna Lawal ya bayyana ƙudirinsa na kawo ƙarshen rashin tsaro a jihar tare da jajanta wa iyalan da ɓarnar ‘yan fashin dajin ta shafa.
“A matsayinsa na shugaba mai tausayi, Gwamna Lawal ya gaggauta samar wa matar da ta rasa muhallin nata gida mai kyau da aka sa wa komai na more rayuwa.
“Ya kuma tabbatar mata da kudirin gwamnatinsa na ciyar da iyalinta abinci da sauran abubuwan bukatu, ta yadda za ta sake gina rayuwarta cikin mutunci da tsaro.
“Bugu da kari, gwamnan ya umarci kwamishinan ilimi, kimiya da fasaha da ya tabbatar da shigar da ‘ya’yanta makaranta cikin gaggawa da kuma samun cikakken tallafin karatu.

“Ya kuma bukaci dukkan hukumomin da abin ya shafa da su ƙara ƙaimi wajen zakulo iyalai marasa galihu da ke fuskantar irin wannan ƙalubale tare da ba su tallafin da ya dace.
“A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Masu Kare Hakkin Bil’adama, Kwamared Salisu Umar, ya bayyana matukar jin daɗinsa kan yadda Gwamnan Jihar Zamfara ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ya kuma yaba da yadda gwamnan ya nuna himma, tare da bayyana cewa wannan ne karon farko da ya ga irin wannan kyakkyawar shugabanci a jihar, inda ya ƙara da cewa kalaman nasa sun yi daidai da ra’ayoyin jama’a, wadanda suka dade suna jiran shugaban da zai riƙa sanya buƙatunsu a gaba.” In ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Fashin dajifaifan bidiyoGwamnan ZamfaraJihar ZamfaraMatamatsuguniMuhalli
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Next Post

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Related

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
Labarai

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

5 hours ago
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana
Labarai

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

7 hours ago
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

19 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

23 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

23 hours ago
Next Post
Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.