• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma’aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

by Leadership Hausa
1 year ago
gwamna

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya kammala biyan bashin haƙƙin ma’aikatan da suka bar aiki na shekara da shekaru, tun daga shekarar 2011, wanda ya kama Naira 9,357,743,281.35.

Idan dai za a iya tunawa, tun a watan Faburairun nan da ya gabata ne gwamnan ya amince da a fara biyan basukan na Garatutin tsoffin ma’aikatan.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa gwamnatin Zamfarar ta riga ta kammala biyan bashin Naira 4,860,613,699.22 rukuni-rukuni 9.

Haka kuma sanarwarta ce an biya tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomin jihar bashin su na Naira 4,497,129,582.13.

  • Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna

 

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Idris ya ce: A jajircewarsa na ganin ya inganta aikin gwamnatin jihar Zamfara, a watan Faburairu Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wani kwamitin da zai tantance duk ilahirin tsaffin ma’aikatan jihar da ba a biya su haƙƙoƙin su ba, tun daga shekarar 2011.

“Ya zuwa yanzu, cikin mutum 3,880 da aka tantance, mutum 2,666 sun karɓi haƙƙoƙin su, wanda ya kai ma Naira 4,860,613,699.22, daga cikin basukan da aka biyo gwamnatocin baya. An biya waɗanda suka bar aiki daga shekarar 2015 zuwa 2024.

“A ɗaya ɓangaren kuma, mutum 3,840 cikin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman Firamare 4,804 da aka tantance sun karɓi haƙƙoƙin su a rukunai 9, wanda ya kai ma kuɗi Naira 4,497,129,582.13. Haƙƙoƙin barin aiki na Garatuti da Ƙananan Hukumomi ke bi ya kai ma Naira 5,688,230,607.20, wanda yanzu haka an biya Naira 4,497,129,582.13. Waɗanda suka bar aiki a tsakanin shekarun 2011- 2021 ne suka amfana.

“A taƙaice dai, ya zuwa yanzu gwamnatin jihar ta biya Tsoffin ma’aikatan jiha da na Ƙananan Hukumomi da ya kai ma Naira 9,357,743,281.35 daga baussukan Naira 13,784,179,513.80 da tsaffin ma’aikatan suka biyo, wato Mutum 6,506, cikin mutum 8,684 da aka tantance. Su ne kuma waɗanda suka bar aiki a tsaknin shekarun 2011- 2024.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.