• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da zaƙulo damammakin da ke tattare da harkar noma a Jihar Gombe ta hanyar tallafawa masana’antun da suka jiɓinci harkar noma, waɗanda ya ce su na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziƙi da zamantakewa.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya ƙaddamar da kamfanin sarrafa taki da sinadaran noma na Al-Yuma a garin Kwadon da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba.

  • Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
  • Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Ya bayyana irin rawar da kamfanin zai taka wajen samar da ayyukan yi da kayan noma don bunƙasa samar da abinci da wadatarsa.

Ya bayyana ƙudurinsa na ci gaba da bunƙasa harkar noma a bisa ƙudurin sabunta fata na Shugaba Tinubu, musamman ƙudurinsa na bunƙasa noma don tabbatar da isasshen abinci a ƙasar nan.

“Kuma tun hawanmu kan karagar mulki a 2019, muke mayar da hankali kan samar da abinci. Domin mun yi imanin cewa ci gabanmu ya ta’allaka ne da noma,” in ji Gwamna Inuwa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Gwamna Inuwa
Wani yanki daga cikin masana’antar

Gwamnan ya ci gaba da cewa, akwai wadatacciyar ƙasa mai faɗin gaske a Gombe, ga kuma yawan al’ummar da sun kai su samar da wadataccen abinci, yana mai jaddada cewa, “Babu dalilin da zai sa Nijeriya ta dogara da shigo da abinci daga ƙasashen waje alhali muna da abin da za mu iya ciyar da kanmu”.

Da ya ke yabawa da irin rawar da ‘yan kasuwa ke takawa wajen rage zaman banza, Gwamna Inuwa ya ce “Duk da cewa samar da ayyukan yi shi ne abu na farko da ya rataya a wuyan ‘yan kasuwa, aikin gwamnati shi ne ta samar da kyakkyawan yanayin haɓaka kasuwancin, don haka a shirye muke mu tallafawa duk wani dan kasuwa da ke son ya kafa kasuwancinsa a Jihar Gombe”.

Ya ce irin nasarorin da Gombe ta samu har sau biyu a fagen sauƙaƙa kasuwanci da kuma samun kyakkyawan matsayi har uku a fannin kyautata tattalin arziki da zamantakewa a matsayin shaida kan ƙudurin gwamnatinsa na samar da yanayi mai aminci don ‘yan kasuwa su ci gaba.

Gwamna Inuwa

Gwamnan ya sanar da kawo karshen rabon tallafin abinci, maimakon hakan ya ce taki za a samar don ƙarfafa gwiwar jama’a su koma gona don magance matsalolin tattalin arziƙi.

Gwamna Inuwa ya sanar da sayan taki tan dubu 200 daga sabon kamfanin na Alyuma don rabawa manoman Jihar Gombe. “Za mu sayi taki don tallafa muku idan kun shirya komawa noma,” in ji shi.

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban Kamfanin taki da sinadaran na Al-Yuma, Alhaji Yusuf Ali Yusuf, wanda ya samu wakilcin Manajan Daraktan Kamfanin, Dakta Faruk Hamza, ya ce kyakkyawan yanayin kasuwanci da gwamnan ya samar a Jihar Gombe ne ya ƙarfafa musu kafa kamfanin a jihar.

Ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya samar da ingantattun manufofi tare da goyon baya daga gwamnatinsa ga ‘yan kasuwa.

Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa bisa kishinsa ga noma, yana mai cewa kyawawan manufofinsa ne suka zaburar da su. “Kokarinka ya taimaka matuƙa wajen kawo wannan kamfani Jihar Gombe, kuma ga shi a ƙarshe aikin ya yi nasara,” in ji shi.

Ya ce kamfanin na da ƙarfin samar da tan dubu 120 na takin zamani kala-kala a duk shekara, “Har ila yau, muna samar da takin da zai dace da kowace irin ƙasa ko amfanin gona,” in ji shi.

Gwamna Inuwa

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Yamaltu Alhaji Abubakar Aliyu, ya godewa Gwamna Inuwa bisa samar da yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali don kafa irin waɗannan kamfanoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Irin takin noman raniNoman ZamaniTsadar kayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano

Next Post

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

Related

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

47 minutes ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

3 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

5 hours ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

6 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

7 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

7 hours ago
Next Post
Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

July 28, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

July 28, 2025
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.