• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da zaƙulo damammakin da ke tattare da harkar noma a Jihar Gombe ta hanyar tallafawa masana’antun da suka jiɓinci harkar noma, waɗanda ya ce su na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziƙi da zamantakewa.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya ƙaddamar da kamfanin sarrafa taki da sinadaran noma na Al-Yuma a garin Kwadon da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba.

  • Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
  • Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Ya bayyana irin rawar da kamfanin zai taka wajen samar da ayyukan yi da kayan noma don bunƙasa samar da abinci da wadatarsa.

Ya bayyana ƙudurinsa na ci gaba da bunƙasa harkar noma a bisa ƙudurin sabunta fata na Shugaba Tinubu, musamman ƙudurinsa na bunƙasa noma don tabbatar da isasshen abinci a ƙasar nan.

“Kuma tun hawanmu kan karagar mulki a 2019, muke mayar da hankali kan samar da abinci. Domin mun yi imanin cewa ci gabanmu ya ta’allaka ne da noma,” in ji Gwamna Inuwa.

Labarai Masu Nasaba

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamna Inuwa
Wani yanki daga cikin masana’antar

Gwamnan ya ci gaba da cewa, akwai wadatacciyar ƙasa mai faɗin gaske a Gombe, ga kuma yawan al’ummar da sun kai su samar da wadataccen abinci, yana mai jaddada cewa, “Babu dalilin da zai sa Nijeriya ta dogara da shigo da abinci daga ƙasashen waje alhali muna da abin da za mu iya ciyar da kanmu”.

Da ya ke yabawa da irin rawar da ‘yan kasuwa ke takawa wajen rage zaman banza, Gwamna Inuwa ya ce “Duk da cewa samar da ayyukan yi shi ne abu na farko da ya rataya a wuyan ‘yan kasuwa, aikin gwamnati shi ne ta samar da kyakkyawan yanayin haɓaka kasuwancin, don haka a shirye muke mu tallafawa duk wani dan kasuwa da ke son ya kafa kasuwancinsa a Jihar Gombe”.

Ya ce irin nasarorin da Gombe ta samu har sau biyu a fagen sauƙaƙa kasuwanci da kuma samun kyakkyawan matsayi har uku a fannin kyautata tattalin arziki da zamantakewa a matsayin shaida kan ƙudurin gwamnatinsa na samar da yanayi mai aminci don ‘yan kasuwa su ci gaba.

Gwamna Inuwa

Gwamnan ya sanar da kawo karshen rabon tallafin abinci, maimakon hakan ya ce taki za a samar don ƙarfafa gwiwar jama’a su koma gona don magance matsalolin tattalin arziƙi.

Gwamna Inuwa ya sanar da sayan taki tan dubu 200 daga sabon kamfanin na Alyuma don rabawa manoman Jihar Gombe. “Za mu sayi taki don tallafa muku idan kun shirya komawa noma,” in ji shi.

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban Kamfanin taki da sinadaran na Al-Yuma, Alhaji Yusuf Ali Yusuf, wanda ya samu wakilcin Manajan Daraktan Kamfanin, Dakta Faruk Hamza, ya ce kyakkyawan yanayin kasuwanci da gwamnan ya samar a Jihar Gombe ne ya ƙarfafa musu kafa kamfanin a jihar.

Ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya samar da ingantattun manufofi tare da goyon baya daga gwamnatinsa ga ‘yan kasuwa.

Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa bisa kishinsa ga noma, yana mai cewa kyawawan manufofinsa ne suka zaburar da su. “Kokarinka ya taimaka matuƙa wajen kawo wannan kamfani Jihar Gombe, kuma ga shi a ƙarshe aikin ya yi nasara,” in ji shi.

Ya ce kamfanin na da ƙarfin samar da tan dubu 120 na takin zamani kala-kala a duk shekara, “Har ila yau, muna samar da takin da zai dace da kowace irin ƙasa ko amfanin gona,” in ji shi.

Gwamna Inuwa

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Yamaltu Alhaji Abubakar Aliyu, ya godewa Gwamna Inuwa bisa samar da yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali don kafa irin waɗannan kamfanoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Irin takin noman raniNoman ZamaniTsadar kayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano

Next Post

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

Related

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

59 minutes ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

2 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

3 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

4 hours ago
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

7 hours ago
Next Post
Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.