ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Kammala Rangadin Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
1 week ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya kammala rangadin kananan hukumomi 34 na jihar inda ya bude wasu ayyukan da gwamnatin sa ta aiwatar da kuma wadanda shugabannin kananan hukumomi suka yi tare da dora harsashin wasu ayyukan.

Rangadin dai Radda ya kwashe kimanin kwana tara yana gudanarwa ya dauki hankali so sai musamman ‘yan adawa inda suka bayyana cewa yakin neman zabe ne yake yi a fakaice.

Barista Mustapha Shitu mashawarcin jam’iyar adawa ta ADC ya bayyana cewa babu abinda gwamnan Dikko Radda ke yi sai yakin neman zaben ta sigar dibara da wasa da hankali al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro

Jam’iyyar adawa ta ADC ta dage cewa babu wani rangadi da bude ayyuka yakin neman zabe ne aka fara saboda gwamnati ta lura al’umma ta juya mata baya.

To, sai dai gwamnan da kansa ya bayyana cewa yanzu ba lokacin yakin neman zabe, inda ya yi kira ga ‘yan siyasa da su gu ji duk wani abu da zai alakanta su da batun siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Gwamnan dai ya fara wannan rangadi a shiryar Funtua inda ya kwashe kwanaki uku yana bi kananan hukumomi domin duba irin ayyukan da shugabannin kananan hukumomi suka asassa da kuma wanda shi ya aiwatar.

Wani abu da ya dora yatsan zargin akan wannan rangadi na gwamna Radda shi ne taron masu ruwa da tsaki na kowace karamar hukumar da ya ziyarta, inda ‘yan adawa ke cewa, wayan aci ne wai an kori kare.

Batutuwan da suka dabaibaye wannan rangadi na gwamna Radda sun hada da ganawa da jama’a musamman ‘ya ‘yan jam’iyyar APC da suka dadai ba su hadu ba.

Kazalika gwamnan Radda yana kai ziyarar ban girma ga masu rike da masarautar gargajiya musamman hakimai na kowace karamar hukuma kafin ya gana da masu ruwa da tsaki sannan ya wuce wajen taron domin kaddamar da ayyukan tallafi.

Wasu kananan hukumomin an ga yadda suka yi kokari wajen gwangwaje al’ummar su da kayan arziki wasu kuma ba yabo ba fallasa, wasu kuma babu wani abin azo a gani.

A karamar hukumar Batsari kuwa an iske shugaban karamar hukumar Hon. Munnir Mu’azu ya yi runton aiki inda ya kasa yin komi daga karshe ya buge da maida ayyukan tsohon shugaban karamar hukumar zuwa na shi.

Duk da haka, wasu kananan hukumomi irin su Safana da Jibia da Charanchi da Mani da Dutsi da Musawa da sauran su, sun yi namijin kokari wajen gwangwaje al’ummar su da ayyuka.

Ya kara da cewa yana fatan kayayyakin da aka rabawa al’umma na tallafi zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki musamman masu kananan sana’o’i a yankunan karkara.

Daga cikin abubuwan da aka samarwa al’umma sun hada da motoci da mashina da kekunan dinki da kudadai da injinan markade da na faci da sauran kayayyakin more rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami’an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami'an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.