ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar
7 months ago
Katsina

Jam’iyyar APC a Jiharr Katsina ta umarci mambobinta su tabbatar da samun nasarar rangadin da Gwamna Dikko Raɗɗa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Shugaban jam’iyyar na jihar, Alhaji Sani Aliyu Daura ya bayar da wannan umarni bayan wani taron kwamitin zartaswar jam’iyyar da aka gudanar a sakatariyar jam’iyyar.

  • Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 
  • Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (3)

Ya ce ziyara zuwa yankunan ƙananan hukumomi 34 a jihar na da nufin duba ayyukan da ƙananan hukumomi suka aiwatar ba don gangamin siyasa ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na jihar ya gargaɗi mambobin jam’iyyar masu neman muƙamai daban-daban su guji ɗaukar nauyin magoya bayansu wajen ɗauka ko nuna fastoci a lokacin rangadin.

Sai dai, Alhaji Sani ya yi cikakken bayani kan shirin rajistar ƴan jam’iyyar, yana mai cewa jami’ai guda 2 za su gudanar da rajistar a kowacce mazaɓa.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Ya buƙaci ‘ya’yan jam’iyyar su mallaki lambar katin shaidar ɗan ƙasa ta NIN wadda ita aka fi buƙata wajen yin rajistar a zamanance.

Ya bayyana cewa jam’iyyar na buƙatar yi wa sama da mambobi miliyan 3 rajista sama da mambobin miliyan 1.5 da aka yi wa rajista a lokacin shirin da ya gabata.

Shi ma da yake jawabi, mataimakin shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bala Abu Musawa ya yi ƙarin haske kan rangadin na gwamna da kuma rajistar mambobin jam’iyyar na zamani.

Alhaji Bala Abu Musawa ya bayyana farin cikin cikinsa bisa ɗimbin magoya bayan jam’iyyar da suka taru a ƙaramar hukumar Faskari, sai dai ya yi gargaɗin cewa jam’iyyar ba za ta lamunci rashin biyayya ba.

Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar a jihar su nuna dattako a lokacin ziyarar aiki ta gwamnan zuwa majalisun ƙananan hukumomi 34 na jihar.

A dukkan ƙananan hukumomin, gwamnan ya gana da manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da na addini da ƴan siyasa da matasa da ƙungiyoyin mata.

A ziyararsa zuwa Malumfashi, Gwamna Dikko Raɗɗa ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi domin ƙarfafa harkokin kasuwanci ga al’umma tare da raba motoci ga jami’an ƙaramar hukumar da jagororin jam’iyyar APC.

Haka zalika a Ƙafur, gwamnan ya ƙaddamar da tallafin jari ga ƴan kasuwa ƙanana dubu ɗaya da ɗari takwas da hamsin da tara, sannan ya bayar da naira dubu talatin-talatin ga wasu mutane dubu ɗaya domin tallafa musa wajen bunƙasa sana’o’insu.

Katsina
Sagir Abubakar
+ postsBio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Barayin Shanu Sun Kashe DPO A Karamar Hukumar Rimi Ta Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Radda Ya Rantsar Da Sabon Mai Shari’a, Khadi Mustapha Salisu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.