ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar
7 months ago
Katsina

Jam’iyyar APC a Jiharr Katsina ta umarci mambobinta su tabbatar da samun nasarar rangadin da Gwamna Dikko Raɗɗa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Shugaban jam’iyyar na jihar, Alhaji Sani Aliyu Daura ya bayar da wannan umarni bayan wani taron kwamitin zartaswar jam’iyyar da aka gudanar a sakatariyar jam’iyyar.

  • Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 
  • Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (3)

Ya ce ziyara zuwa yankunan ƙananan hukumomi 34 a jihar na da nufin duba ayyukan da ƙananan hukumomi suka aiwatar ba don gangamin siyasa ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na jihar ya gargaɗi mambobin jam’iyyar masu neman muƙamai daban-daban su guji ɗaukar nauyin magoya bayansu wajen ɗauka ko nuna fastoci a lokacin rangadin.

Sai dai, Alhaji Sani ya yi cikakken bayani kan shirin rajistar ƴan jam’iyyar, yana mai cewa jami’ai guda 2 za su gudanar da rajistar a kowacce mazaɓa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ya buƙaci ‘ya’yan jam’iyyar su mallaki lambar katin shaidar ɗan ƙasa ta NIN wadda ita aka fi buƙata wajen yin rajistar a zamanance.

Ya bayyana cewa jam’iyyar na buƙatar yi wa sama da mambobi miliyan 3 rajista sama da mambobin miliyan 1.5 da aka yi wa rajista a lokacin shirin da ya gabata.

Shi ma da yake jawabi, mataimakin shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bala Abu Musawa ya yi ƙarin haske kan rangadin na gwamna da kuma rajistar mambobin jam’iyyar na zamani.

Alhaji Bala Abu Musawa ya bayyana farin cikin cikinsa bisa ɗimbin magoya bayan jam’iyyar da suka taru a ƙaramar hukumar Faskari, sai dai ya yi gargaɗin cewa jam’iyyar ba za ta lamunci rashin biyayya ba.

Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar a jihar su nuna dattako a lokacin ziyarar aiki ta gwamnan zuwa majalisun ƙananan hukumomi 34 na jihar.

A dukkan ƙananan hukumomin, gwamnan ya gana da manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da na addini da ƴan siyasa da matasa da ƙungiyoyin mata.

A ziyararsa zuwa Malumfashi, Gwamna Dikko Raɗɗa ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi domin ƙarfafa harkokin kasuwanci ga al’umma tare da raba motoci ga jami’an ƙaramar hukumar da jagororin jam’iyyar APC.

Haka zalika a Ƙafur, gwamnan ya ƙaddamar da tallafin jari ga ƴan kasuwa ƙanana dubu ɗaya da ɗari takwas da hamsin da tara, sannan ya bayar da naira dubu talatin-talatin ga wasu mutane dubu ɗaya domin tallafa musa wajen bunƙasa sana’o’insu.

Katsina
Sagir Abubakar
+ postsBio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.