ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina

by Sagir Abubakar
6 months ago
Katsina

Jam’iyyar APC a Jiharr Katsina ta umarci mambobinta su tabbatar da samun nasarar rangadin da Gwamna Dikko Raɗɗa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Shugaban jam’iyyar na jihar, Alhaji Sani Aliyu Daura ya bayar da wannan umarni bayan wani taron kwamitin zartaswar jam’iyyar da aka gudanar a sakatariyar jam’iyyar.

  • Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 
  • Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (3)

Ya ce ziyara zuwa yankunan ƙananan hukumomi 34 a jihar na da nufin duba ayyukan da ƙananan hukumomi suka aiwatar ba don gangamin siyasa ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na jihar ya gargaɗi mambobin jam’iyyar masu neman muƙamai daban-daban su guji ɗaukar nauyin magoya bayansu wajen ɗauka ko nuna fastoci a lokacin rangadin.

Sai dai, Alhaji Sani ya yi cikakken bayani kan shirin rajistar ƴan jam’iyyar, yana mai cewa jami’ai guda 2 za su gudanar da rajistar a kowacce mazaɓa.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Ya buƙaci ‘ya’yan jam’iyyar su mallaki lambar katin shaidar ɗan ƙasa ta NIN wadda ita aka fi buƙata wajen yin rajistar a zamanance.

Ya bayyana cewa jam’iyyar na buƙatar yi wa sama da mambobi miliyan 3 rajista sama da mambobin miliyan 1.5 da aka yi wa rajista a lokacin shirin da ya gabata.

Shi ma da yake jawabi, mataimakin shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bala Abu Musawa ya yi ƙarin haske kan rangadin na gwamna da kuma rajistar mambobin jam’iyyar na zamani.

Alhaji Bala Abu Musawa ya bayyana farin cikin cikinsa bisa ɗimbin magoya bayan jam’iyyar da suka taru a ƙaramar hukumar Faskari, sai dai ya yi gargaɗin cewa jam’iyyar ba za ta lamunci rashin biyayya ba.

Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar a jihar su nuna dattako a lokacin ziyarar aiki ta gwamnan zuwa majalisun ƙananan hukumomi 34 na jihar.

A dukkan ƙananan hukumomin, gwamnan ya gana da manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da na addini da ƴan siyasa da matasa da ƙungiyoyin mata.

A ziyararsa zuwa Malumfashi, Gwamna Dikko Raɗɗa ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi domin ƙarfafa harkokin kasuwanci ga al’umma tare da raba motoci ga jami’an ƙaramar hukumar da jagororin jam’iyyar APC.

Haka zalika a Ƙafur, gwamnan ya ƙaddamar da tallafin jari ga ƴan kasuwa ƙanana dubu ɗaya da ɗari takwas da hamsin da tara, sannan ya bayar da naira dubu talatin-talatin ga wasu mutane dubu ɗaya domin tallafa musa wajen bunƙasa sana’o’insu.

Katsina
Sagir Abubakar
+ postsBio
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnatin Jihar Katsina Na Shirin Samar Da Tsarin Kula Da Masu Cutar Daji
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Barayin Shanu Sun Kashe DPO A Karamar Hukumar Rimi Ta Jihar Katsina
  • Sagir Abubakar
    https://hausa.leadership.ng/author/sagir-abubakar/
    Gwamnan Radda Ya Rantsar Da Sabon Mai Shari’a, Khadi Mustapha Salisu

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.