ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Kammala Rangadin Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
9 months ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya kammala rangadin kananan hukumomi 34 na jihar inda ya bude wasu ayyukan da gwamnatin sa ta aiwatar da kuma wadanda shugabannin kananan hukumomi suka yi tare da dora harsashin wasu ayyukan.

Rangadin dai Radda ya kwashe kimanin kwana tara yana gudanarwa ya dauki hankali so sai musamman ‘yan adawa inda suka bayyana cewa yakin neman zabe ne yake yi a fakaice.

Barista Mustapha Shitu mashawarcin jam’iyar adawa ta ADC ya bayyana cewa babu abinda gwamnan Dikko Radda ke yi sai yakin neman zaben ta sigar dibara da wasa da hankali al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro

Jam’iyyar adawa ta ADC ta dage cewa babu wani rangadi da bude ayyuka yakin neman zabe ne aka fara saboda gwamnati ta lura al’umma ta juya mata baya.

To, sai dai gwamnan da kansa ya bayyana cewa yanzu ba lokacin yakin neman zabe, inda ya yi kira ga ‘yan siyasa da su gu ji duk wani abu da zai alakanta su da batun siyasa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Gwamnan dai ya fara wannan rangadi a shiryar Funtua inda ya kwashe kwanaki uku yana bi kananan hukumomi domin duba irin ayyukan da shugabannin kananan hukumomi suka asassa da kuma wanda shi ya aiwatar.

Wani abu da ya dora yatsan zargin akan wannan rangadi na gwamna Radda shi ne taron masu ruwa da tsaki na kowace karamar hukumar da ya ziyarta, inda ‘yan adawa ke cewa, wayan aci ne wai an kori kare.

Batutuwan da suka dabaibaye wannan rangadi na gwamna Radda sun hada da ganawa da jama’a musamman ‘ya ‘yan jam’iyyar APC da suka dadai ba su hadu ba.

Kazalika gwamnan Radda yana kai ziyarar ban girma ga masu rike da masarautar gargajiya musamman hakimai na kowace karamar hukuma kafin ya gana da masu ruwa da tsaki sannan ya wuce wajen taron domin kaddamar da ayyukan tallafi.

Wasu kananan hukumomin an ga yadda suka yi kokari wajen gwangwaje al’ummar su da kayan arziki wasu kuma ba yabo ba fallasa, wasu kuma babu wani abin azo a gani.

A karamar hukumar Batsari kuwa an iske shugaban karamar hukumar Hon. Munnir Mu’azu ya yi runton aiki inda ya kasa yin komi daga karshe ya buge da maida ayyukan tsohon shugaban karamar hukumar zuwa na shi.

Duk da haka, wasu kananan hukumomi irin su Safana da Jibia da Charanchi da Mani da Dutsi da Musawa da sauran su, sun yi namijin kokari wajen gwangwaje al’ummar su da ayyuka.

Ya kara da cewa yana fatan kayayyakin da aka rabawa al’umma na tallafi zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki musamman masu kananan sana’o’i a yankunan karkara.

Daga cikin abubuwan da aka samarwa al’umma sun hada da motoci da mashina da kekunan dinki da kudadai da injinan markade da na faci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami’an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami'an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.