ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Kammala Rangadin Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
6 months ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya kammala rangadin kananan hukumomi 34 na jihar inda ya bude wasu ayyukan da gwamnatin sa ta aiwatar da kuma wadanda shugabannin kananan hukumomi suka yi tare da dora harsashin wasu ayyukan.

Rangadin dai Radda ya kwashe kimanin kwana tara yana gudanarwa ya dauki hankali so sai musamman ‘yan adawa inda suka bayyana cewa yakin neman zabe ne yake yi a fakaice.

Barista Mustapha Shitu mashawarcin jam’iyar adawa ta ADC ya bayyana cewa babu abinda gwamnan Dikko Radda ke yi sai yakin neman zaben ta sigar dibara da wasa da hankali al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro

Jam’iyyar adawa ta ADC ta dage cewa babu wani rangadi da bude ayyuka yakin neman zabe ne aka fara saboda gwamnati ta lura al’umma ta juya mata baya.

To, sai dai gwamnan da kansa ya bayyana cewa yanzu ba lokacin yakin neman zabe, inda ya yi kira ga ‘yan siyasa da su gu ji duk wani abu da zai alakanta su da batun siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnan dai ya fara wannan rangadi a shiryar Funtua inda ya kwashe kwanaki uku yana bi kananan hukumomi domin duba irin ayyukan da shugabannin kananan hukumomi suka asassa da kuma wanda shi ya aiwatar.

Wani abu da ya dora yatsan zargin akan wannan rangadi na gwamna Radda shi ne taron masu ruwa da tsaki na kowace karamar hukumar da ya ziyarta, inda ‘yan adawa ke cewa, wayan aci ne wai an kori kare.

Batutuwan da suka dabaibaye wannan rangadi na gwamna Radda sun hada da ganawa da jama’a musamman ‘ya ‘yan jam’iyyar APC da suka dadai ba su hadu ba.

Kazalika gwamnan Radda yana kai ziyarar ban girma ga masu rike da masarautar gargajiya musamman hakimai na kowace karamar hukuma kafin ya gana da masu ruwa da tsaki sannan ya wuce wajen taron domin kaddamar da ayyukan tallafi.

Wasu kananan hukumomin an ga yadda suka yi kokari wajen gwangwaje al’ummar su da kayan arziki wasu kuma ba yabo ba fallasa, wasu kuma babu wani abin azo a gani.

A karamar hukumar Batsari kuwa an iske shugaban karamar hukumar Hon. Munnir Mu’azu ya yi runton aiki inda ya kasa yin komi daga karshe ya buge da maida ayyukan tsohon shugaban karamar hukumar zuwa na shi.

Duk da haka, wasu kananan hukumomi irin su Safana da Jibia da Charanchi da Mani da Dutsi da Musawa da sauran su, sun yi namijin kokari wajen gwangwaje al’ummar su da ayyuka.

Ya kara da cewa yana fatan kayayyakin da aka rabawa al’umma na tallafi zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki musamman masu kananan sana’o’i a yankunan karkara.

Daga cikin abubuwan da aka samarwa al’umma sun hada da motoci da mashina da kekunan dinki da kudadai da injinan markade da na faci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami’an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami'an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.