ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Kammala Rangadin Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
7 months ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya kammala rangadin kananan hukumomi 34 na jihar inda ya bude wasu ayyukan da gwamnatin sa ta aiwatar da kuma wadanda shugabannin kananan hukumomi suka yi tare da dora harsashin wasu ayyukan.

Rangadin dai Radda ya kwashe kimanin kwana tara yana gudanarwa ya dauki hankali so sai musamman ‘yan adawa inda suka bayyana cewa yakin neman zabe ne yake yi a fakaice.

Barista Mustapha Shitu mashawarcin jam’iyar adawa ta ADC ya bayyana cewa babu abinda gwamnan Dikko Radda ke yi sai yakin neman zaben ta sigar dibara da wasa da hankali al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Gwamna Raɗɗa Ya Yi Rangadi Ga Dukkanin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro

Jam’iyyar adawa ta ADC ta dage cewa babu wani rangadi da bude ayyuka yakin neman zabe ne aka fara saboda gwamnati ta lura al’umma ta juya mata baya.

To, sai dai gwamnan da kansa ya bayyana cewa yanzu ba lokacin yakin neman zabe, inda ya yi kira ga ‘yan siyasa da su gu ji duk wani abu da zai alakanta su da batun siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

Gwamnan dai ya fara wannan rangadi a shiryar Funtua inda ya kwashe kwanaki uku yana bi kananan hukumomi domin duba irin ayyukan da shugabannin kananan hukumomi suka asassa da kuma wanda shi ya aiwatar.

Wani abu da ya dora yatsan zargin akan wannan rangadi na gwamna Radda shi ne taron masu ruwa da tsaki na kowace karamar hukumar da ya ziyarta, inda ‘yan adawa ke cewa, wayan aci ne wai an kori kare.

Batutuwan da suka dabaibaye wannan rangadi na gwamna Radda sun hada da ganawa da jama’a musamman ‘ya ‘yan jam’iyyar APC da suka dadai ba su hadu ba.

Kazalika gwamnan Radda yana kai ziyarar ban girma ga masu rike da masarautar gargajiya musamman hakimai na kowace karamar hukuma kafin ya gana da masu ruwa da tsaki sannan ya wuce wajen taron domin kaddamar da ayyukan tallafi.

Wasu kananan hukumomin an ga yadda suka yi kokari wajen gwangwaje al’ummar su da kayan arziki wasu kuma ba yabo ba fallasa, wasu kuma babu wani abin azo a gani.

A karamar hukumar Batsari kuwa an iske shugaban karamar hukumar Hon. Munnir Mu’azu ya yi runton aiki inda ya kasa yin komi daga karshe ya buge da maida ayyukan tsohon shugaban karamar hukumar zuwa na shi.

Duk da haka, wasu kananan hukumomi irin su Safana da Jibia da Charanchi da Mani da Dutsi da Musawa da sauran su, sun yi namijin kokari wajen gwangwaje al’ummar su da ayyuka.

Ya kara da cewa yana fatan kayayyakin da aka rabawa al’umma na tallafi zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki musamman masu kananan sana’o’i a yankunan karkara.

Daga cikin abubuwan da aka samarwa al’umma sun hada da motoci da mashina da kekunan dinki da kudadai da injinan markade da na faci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami’an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

CCB Na Binciken Tsoffin Ministoci Da Manyan Jami'an Gwamnati Kan Cin Hanci Da Rashawa 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.