• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 

by Sulaiman
1 year ago
Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Gwamnatin Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, ta shirya tsaf don kaddamar da kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke karamar hukumar Soba a  yankin Zaria da ke Jihar.

Hakan na kunshe ne acikin wata tattaunawa da manema labarai da shugaban kwalejin, Dakta Yusuf Bello ya yi ranar Litinin, 9 ga watan Satumba, 2024 gabanin kaddamar da Kwalejin a harabar Kwalejin da ke Pambegua.
  • Gine-gine Da Zubar Da Shara A Magudanun Ruwa Ke Haifar Da Ambaliya A Kaduna – Kwamiti
  • Zanga-zanga: Gwamna Uba Sani Ya Musanta Sanya Dokar Hana Fita A Kaduna
Kwalejin Ta Pambegua, daya ce daga cikin sansanonin kwalejojin da ke da babban sansani a Asibitin Dantshoho, a birnin Kaduna, karkashin shugabancin Dakta Yusuf Bello.
Sansanonin Kwalejin sun hada da Kwalejin Koyon aikin jinya ta Asibitin Dantsoho, Tudun wada, da ke cikin birnin Kaduna; Kwalejin Koyon aikin jinya, Kafanchan, da ke kudancin Kaduna, da Kwalejin Koyon aikin jinya, Pambegua da ke yankin Zaria.
Kwalejin ta samu amincewar hukumomin da ke kula da manyan makarantun kiwon lafiya, da hukumar kula da manyan makarantun kimiyya da fasaha (NBTE) don gudanar da karatuttuka a bangaren aikin jinya na shekaru hudu a jere (ND-HND Nursing), ungozoma (Basic Midwifery) da General Nursing.
Dakta Bello ya jinjina wa al’ummar Pambegua bisa namijin kokarinsu da aljihunsu, da karfinsu wajen ganin an samu damar kaddamar da wannan kwalejin a yankinsu, har ta kuma fara aiki.
Shugaban ya kuma sake mika godiyarsa ta musamman ga Gwamna Uba Sani kan kishinsa ga ci gaban al’ummar Kaduna baki daya.
Tun da farko, Hakimin Pambegua, Karfen Dawakin Zazzau, Sufyan Sani Usman, ya jinjina wa Gwamna Uba, bisa kafa irin wannan kwalejin a yankin, inda ya ce, kwalejin ba al’ummar Pambegua kadai ce za ta amfanar ba, har da yankin Zaria da Jihar Kaduna baki daya.
Hakimin ya kuma gode wa Dakta Bello Yusuf wajen ganin wannan Kwalejin ta samu nasarar kafuwa.
Shugaban kwamitin kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke Pambegua, Alhaji Haruna Ahmad, ya kuma yaba da irin gudunmawar da al’umma suka bayar, da suka hada da gyare-gyare da kuma sayan kayan aiki domin tabbatar da gudanar da ayyuka a kwalejin.
Ya kuma yabawa gwamnati bisa yadda ta tabbatar da aikin da aka dade ana jira a yankin tare da tabbatar da cewa al’ummar karkara za su ci gajiyar kokarin gwamnati.
Shi ma Akanta Janar na Jihar Kaduna, kuma tsohon shugaban karamar hukuma, Alhaji Bashir Suleiman Zuntu, ya yaba da irin nasarorin da gwamnati ta samu, ya kuma yi fatan samun nasarar gudanar da ayyuka a kwalejin ta Pambegua.
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.