• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bai wa kungiyar Kiristoci ta kasa a jihar (CAN) tallafin naira miliyan 25 domin gina masaukin baki na kungiyar tare da karin wasu naira miliyan 15 don shingace cibiyar da sauran ayyuka.

 

Tallafin kudin na zuwa ne a lokacin da mambobin Ƙungiyar Kiristoci a Jihar Gombe suka kai wa gwamnan ziyarar bangirma ta sabuwar shekara.

  • 2023: Mai Binciken Kudin PDP Da Wasu Jiga-jigan Jam’iyyar Sun Koma NNPP A Gombe

Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, CAN reshen Jihar Gombe, Rev. Fr. Joseph Alphonsus Shinga yayin ziyarar ya ce mabiya Addinin Kirista a jihar su na alfahari da irin ayyukan da Gwamnan yake yi a fannin samar da ababen more rayuwa a sassa masu muhimmanci na tattalin arzikin jihar, yana mai jaddada cewa idan ya sake samun dama a karo na biyu, jihar za ta shiga wani sabon salo na ci gaba da wadata.

 

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Shinga ya kuma yaba da irin goyon bayan da Gwamna ke bai wa kungiyar CAN, yana mai cewa gwamnan yana bin Kiristocin jihar bashi na ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin sa, saboda halayen sa ababen koyi.

 

Ya godewa Gwamnan bisa daukar nauyin Kiristoci 33 da suka yi aikin ibada a kasar Isra’ila da Jordan a 2022, ya kuma buƙaci a ci gaba da wannan tallafi.

 

Sai ya yi kira ga Gwamna Inuwa Yahaya, ya taimakawa kungiyar wajen samar da ruwan sha ga cibiyar ta CAN, ya kuma bukaci tallafin kudi don gina masaukin baki na kungiyar wanda gwamnatinsa ta taimaka wajen ginata ta hanyar tallafin daya bayar a baya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya godewa al’ummar Kiristocin jihar bisa hadin kan da suke bai wa jihar wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, musamman idan aka kwatanta da kalubalen tsaron da jihohin dake shiyyar Arewa maso Gabas ke fuskanta da sauran su.

 

Ya ce saboda zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a jihar ya sa gwamnatinsa ke iya gudanar da ayyuka don tabbatar da ci gaban al’umma da bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa, don haka ya bukaci al’ummar jihar su zamto masu kishi da kiyaye duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, a yayin bikin Kirsimeti, gwamnatin sa ta bada tallafin kuɗi fiye da Naira miliyan 90 domin tallafawa al’ummar Kirista a jihar wajen gudanar da bukukuwan su cikin sauƙi duba da halin da tattalin arziƙin ƙasar ke ciki.

 

Ya kuma sanar da kyautar Naira miliyan 10 ga Kiristocin a matsayin goron sabuwar shekara, inda aka ware Naira miliyan 5 ga mata da kuma wasu miliyan biyar ga maza.

 

“Hakazalika dangane da bukatar ku ta tallafi a harkar samar da ruwan sha a cibiyar ta CAN, kamar yadda kuka sani muna kan aikin fadada shirin samar da ruwan sha na Gombe, kuma na yi imanin cewa kwanan nan kun ga Ministan Albarkatun Ruwa ya zo ya kaddamar da aikin inda gwamnati ke kashe fiye da Naira biliyan 11.68 don samar da ruwan sha ga al’ummar da aka yi watsi da ita, musamman ma yankunan Tunfure har zuwa cibiyar taro ta ƙasa da ƙasa da kewaye”.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin kira ga al’ummar jihar su karbi katin zaben na dindindin don yun amfani da ‘yancin su su zabi ‘yan takaran da suke so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

Next Post

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

12 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

13 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

18 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

20 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

21 hours ago
Next Post
2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi - Gwamna Bala

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.