• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bai wa kungiyar Kiristoci ta kasa a jihar (CAN) tallafin naira miliyan 25 domin gina masaukin baki na kungiyar tare da karin wasu naira miliyan 15 don shingace cibiyar da sauran ayyuka.

 

Tallafin kudin na zuwa ne a lokacin da mambobin Ƙungiyar Kiristoci a Jihar Gombe suka kai wa gwamnan ziyarar bangirma ta sabuwar shekara.

  • 2023: Mai Binciken Kudin PDP Da Wasu Jiga-jigan Jam’iyyar Sun Koma NNPP A Gombe

Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, CAN reshen Jihar Gombe, Rev. Fr. Joseph Alphonsus Shinga yayin ziyarar ya ce mabiya Addinin Kirista a jihar su na alfahari da irin ayyukan da Gwamnan yake yi a fannin samar da ababen more rayuwa a sassa masu muhimmanci na tattalin arzikin jihar, yana mai jaddada cewa idan ya sake samun dama a karo na biyu, jihar za ta shiga wani sabon salo na ci gaba da wadata.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Shinga ya kuma yaba da irin goyon bayan da Gwamna ke bai wa kungiyar CAN, yana mai cewa gwamnan yana bin Kiristocin jihar bashi na ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin sa, saboda halayen sa ababen koyi.

 

Ya godewa Gwamnan bisa daukar nauyin Kiristoci 33 da suka yi aikin ibada a kasar Isra’ila da Jordan a 2022, ya kuma buƙaci a ci gaba da wannan tallafi.

 

Sai ya yi kira ga Gwamna Inuwa Yahaya, ya taimakawa kungiyar wajen samar da ruwan sha ga cibiyar ta CAN, ya kuma bukaci tallafin kudi don gina masaukin baki na kungiyar wanda gwamnatinsa ta taimaka wajen ginata ta hanyar tallafin daya bayar a baya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya godewa al’ummar Kiristocin jihar bisa hadin kan da suke bai wa jihar wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, musamman idan aka kwatanta da kalubalen tsaron da jihohin dake shiyyar Arewa maso Gabas ke fuskanta da sauran su.

 

Ya ce saboda zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a jihar ya sa gwamnatinsa ke iya gudanar da ayyuka don tabbatar da ci gaban al’umma da bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa, don haka ya bukaci al’ummar jihar su zamto masu kishi da kiyaye duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, a yayin bikin Kirsimeti, gwamnatin sa ta bada tallafin kuɗi fiye da Naira miliyan 90 domin tallafawa al’ummar Kirista a jihar wajen gudanar da bukukuwan su cikin sauƙi duba da halin da tattalin arziƙin ƙasar ke ciki.

 

Ya kuma sanar da kyautar Naira miliyan 10 ga Kiristocin a matsayin goron sabuwar shekara, inda aka ware Naira miliyan 5 ga mata da kuma wasu miliyan biyar ga maza.

 

“Hakazalika dangane da bukatar ku ta tallafi a harkar samar da ruwan sha a cibiyar ta CAN, kamar yadda kuka sani muna kan aikin fadada shirin samar da ruwan sha na Gombe, kuma na yi imanin cewa kwanan nan kun ga Ministan Albarkatun Ruwa ya zo ya kaddamar da aikin inda gwamnati ke kashe fiye da Naira biliyan 11.68 don samar da ruwan sha ga al’ummar da aka yi watsi da ita, musamman ma yankunan Tunfure har zuwa cibiyar taro ta ƙasa da ƙasa da kewaye”.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin kira ga al’ummar jihar su karbi katin zaben na dindindin don yun amfani da ‘yancin su su zabi ‘yan takaran da suke so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

Next Post

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

2 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

4 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

6 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

7 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

8 hours ago
Next Post
2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi - Gwamna Bala

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.