Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gwamnan Gombe Ya Taya Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi Murnar Lashe Zabe

Yayin Da A Ke Rantsar Da Su A Yau Litinin

by Khalid Idris Doya
December 21, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Gwamnan Gombe
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan jihar Gombe Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi 11 da mataimakansu tare da Kansiloli 114 murnar lashe zabe, yana mai kira a gare su da su dauki zaben su da aka yi a matsayin wata dama ta hidimta wa al’ummominsu, jihar da ma kasa.

A dai karshen mako ne aka gudanar da zaben kananan hukumomi na jihar wanda jam’iyyar APC ta lashe dukkanin kujerun kamar yadda hukumomin zabe suka shaida.

samndaads

Bayan ayyana wadanda suka ci nasara a zaben da shugaban hukumar zabe ta jihar Gombe GOSIEC, Alhaji Sa’idu Shehu Awak ya yi ne kuma gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya jam’iyyar APC murna game da nasara da jam’iyyar ta samu a yayin zaben.

Gwamnan na taya jam’iyyar sa da ‘yan takararta murna ne ta cikin sanarwar da Ismaila Uba Misilli, babban mai taimakawa gwamnan kan harkokin yada labarai da hulda da ‘yan jaridu, Inuwa ya nuna farin cikinsa bisa gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali ba tare wani tashin hankali ba.

Sai ya taya wadanda aka zaba murna inda ya ce “ku dauki wannan nasara a matsayin damace da kuka samu don ku hidimtawa al’umma, ku yi iya kokarin ku don cimma kwarin gwiwa da ake da shi akan ku.”

Gwamna Inuwa Yahaya wanda jaddada muhimmancin kananan hukumomi sannan ya bukaci zababbun shugabannin da su aiwatar da shugabanci na gari da zai kai ga bunkasa rayuwar al’umma, karkashin kudirin gwamnatin jam’iyyar APC a jihar Gombe.

Idan za a iya tunawa, hukumar zabe ta jihar Gombe ta sanar da nasarar jam’iyyar APC a zaben kananan hukumomi a dukkanin matakai kama daga Shugabanni 11 da Kansiloli 114.

A wani mataki makamancin wannan, Gwamnatin jihar Gombe ta sanar da cewa a yau Litinin za ta rantsar da sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi 11 inda su kuma za su rantsar da mataimakansu da kansilolin da suke karkashin kowace karamar.

A sanarwar da Sakataren Gwamnatin jihar Ibrahim Abubakar Njodi ya fitar, ya sanar da cewa gwamnan jihar Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya zai rantsar da zababbun shugabannin kananan hukumomin.

Ya ce, bikin rantsarwar zai gudana ne da karfe 9 na safiya a dakin taro na gidan Gwamnatin. Ya umarci a bi matakin kariya daga Korona yayin taron rantsuwar.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Muka Sabunta Sana’ar Walda Domin Magance Zaman Kashe Wando – Sunusi Safiyanu

Next Post

Jami’ar Umaru Musa Za Ta Bai Wa Malamanta Bashin Motoci

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post
Jami’ar Umaru Musa Za Ta Bai Wa Malamanta Bashin Motoci

Jami’ar Umaru Musa Za Ta Bai Wa Malamanta Bashin Motoci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version