• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Bayar Da Umarnin Fara Sabon Gwaji Kan Irin Masara Na ‘Tela Maize’

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnati Ta Bayar Da Umarnin Fara Sabon Gwaji Kan Irin Masara Na ‘Tela Maize’
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Bunkasa Tsirrai Ta Kasa ‘National Biotechnology Debelopment Agency (NBDA)’ ta bayana cewa a halin yanzu an fara wani zagaye na gwajin sabon irin masara na ‘TELA Maize’ a wasu jihohin Nijeriya.

Mataimakiyar Shugabar Hukumar, Dakta Rose Gidado, ta bayyana haka a tattaunawarta da manema labarai ranar Laraba a Legas.

  • Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani
  • Kananan Manoma 31,666 Sun Samu Tallafin Noma Naira Biliyan 5.9 – CBN

Ta ce, manoma za su fara shuka wanan Iri na ‘Tela Maize’ a wannan damunan da muke ciki.

An samar da Tela Maize ne ta hanyar bincike na zamani da ake kira ‘Genetically Modified Organisms (GMO)’ yana kuma da karfin jure wa farmakin kwari da kuma jure wa karancin ruwan sama.

A shekarar 2021 ne gwamnatin tarayyar ta hannun hukumar NBDA ta bayar da izinin cigaba da noma masara a filin Allah saboda ingancinsa kuma baya cutar da muhalli.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Cibiyar Binciken Aikin Gona (IAR) ta Jami’ar ABU ta samar da irin tare da hadin gwiwar Hukumar Binciken Aikin Gona ta Afrika (AATF), da kuma Hukumar Bunkasa Tsirrar (NBDA).

Dakta Gidado ta kuma lura da cewa a halin yanzu IAR da ke Zariya ce gwamnati tarayya ta ba izinin samar da Irin, ta kuma fara rarraba wa manoma Irin masara a yankunan arewacin kasar nan don nomawa a damunan bana.

Ta ce, za a yi sabon gwajin gwajin masarar ne har sau biyu, za a yi a shekarar 2022 da shekarar 2023 kafin a bayar da izinin samar da shi gadan-gadan don manoma gaba daya a fadin Nijeriya.

Ta kara da cewa, a halin yanzu tuni aka fara amfani da irin masarar Tela Maize a wasu jihohi kamar Adamawa, Kaduna, Kano da Jigawa.

Dakta Gidado ta ce irin Tela Maize yana iya jure farmakin kwari kamar (fall armyworm da stem borers) yana kuma jure rashin issashen ruwa sama.

Ta kuma bayana cewa, Nijeriya na daga cikin kasashe 6 a Afrika da suka rungumi Tela Maize, kasashen sun kuma hada da Kenya, Uganda, Tanzania, Ethiopia, Mozambikue da kuma Afrika ta Kudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiIrin masara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Da Orbih Sun Gana Da Gwamna Wike A Jihar Ribas

Next Post

Amurka Za Ta Yi Amai Ta Lashe Game Da Dokar Dake Shafar Yankin Xinjiang Da Ta Zartar

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

4 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

4 weeks ago
Next Post
Amurka Za Ta Yi Amai Ta Lashe Game Da Dokar Dake Shafar Yankin Xinjiang Da Ta Zartar

Amurka Za Ta Yi Amai Ta Lashe Game Da Dokar Dake Shafar Yankin Xinjiang Da Ta Zartar

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.