• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Shure Yarjejeniyarmu, Yanzu Ba Mu San Alkiblarmu Ba – IKMAN

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
in Rahotonni
0
Gwamnati Ta Shure Yarjejeniyarmu, Yanzu Ba Mu San Alkiblarmu Ba – IKMAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

ALHAJI DAHIRU BUBA MADAGALI, shi ne shugaban kungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu ta kasa (IKMAN), reshen jihohin Adamawa da Taraba.

Wakilinmu na Jihar Adamawa, MUHAMMAD SHAFI’U SALE ya tattauna da shi kafin karin kudin mai da canja tsarin NNPC, kan matsalolin da suka dabaibaye harkokin man fetur, karancinsa, karkatar da shi, da wahalhalun da jama’a ke sha.

  • Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas
  • Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

Ga yadda hirar ta kasance kamar haka:

Masu karatunmu za su so ka gabatar musu da kanka.

Sunana Alhaji Dahiru Buba, haifaffen Madagali. Ina zaune a Yola kusan shekarau 30, ina gudanar da harkokin kasuwancina har Allah ya kai ni wannan lokacin da aka zabe ni shugaban IKMAN a jihohin Adamawa da Taraba.

Ina shugabancin jihohi da yawa ne, saboda bisa dokar man fetur ana bin deport ne ba jiha ba, kamar Adamawa an hada ta da Taraba, yayin da Gombe aka hada ta da Bauchi, Borno an hadata da Yobe, to haka ne ayyukanmu na kasuwancin gashinkai ke bin tsarin dokar Nijriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Ka yi maganar cin gashinkai, wani karin haske za ka yi game da gashinkan da kake nufi?

A dokance, kafin ka gina gidan mai, sai ka tuntunbi gwamnati, sannan za ka kira jami’an ‘yan sanda su tabbatar da filin wurin yana da kyau, haka kuma za ka kira jami’an kashe gobara su je su duba wurin ta yadda ba za a samu gobarar da za ta addabi jama’a ba, za ka tafi hukumar tsara birane da kuma ma’aikatan muhalli duk su saka maka hannu da sauran su.

Daga nan kuma za ka soma zuwa sashin hukumar kula da man fetur (DPR) domin amince maka ka gina gidan mai.

Idan ka kammala gina gidan mai, hukumar DPR za su baka lassis (takardan amincewa), sai ka rumgumi lassis da sauran takardunka ka tafi NNPC, ka je ka shiga yarjejeniya tsakaninka da gwamnati da shugaban kamfanin mai na kasa (NNPC) da sakataren NNPC, za ku sa hannu a kan yadda za a baka mai.

Idan kana da tanki guda hudu wanda ya kai 45, shi ne za a ci gaba da baka kowace rana, kai za ka yi yadda za ka sayar da shi, sannan kuma a sake baka wani.

Sai dai kuma a yanzu gwamnati ta rushe wannan yarjejeniya, inda a yanzu haka ba mu san alkiblarmu ba. A baya, za ka shugaban deport ke sayar da man a madadin NNPC, amma a yanzu gaba daya komi ya koma Abuja hannun shugaban NNPC.

Idan kana da gidan mai guda daya kuma banki yake taimaka maka da kudaden kawo man, sannan kuma an ce yau a Nijeriya mutum daya ne zai sa maka hannu kafin ka samu mai dole a samu matsala.

Wannan shi ne dalillin da ba ma samun mai, wanda ta kai muna sayan man daga hannun wasu da ake takaita sunansu da MOMAN, kuma suna sayar manada mai da tsada.

A baya ana sayar mana da man kan Naira 166, amma yanzu an kara ana sayarwa a boye wanda kudin mai ya koma 185.

A takaice dai a halin da muke ciki yanzu, maganar mai babu wanda zai gaya maka tabbacin ga halin da ake ciki, domin maganar mai ta zama ba ta da alkibla gaba daya.

Wato rashin aiki da yarjejeniyar da ke tsakaninku da gwamnatin tarayya ya haifar da karancin mai, wanda hakan ya jefa ‘yan Nijeriya halin da suka samu kansu a yanzu na karancin mai.

NNPC yana cewa yana raba mai kamar yadda ya saba, ku kuma kuna cewa ba a ba ku man, ina man ke shiga?

Wasu ‘yan kalilan mutane ne ake ba su, idan an ce maka ana ba da mai, ana bai wa A.A Rano da Shafa da Mai Kifi da dan Marna da Shema kadai, to wadannan kalilan mutane idan sun yi yawa su kai mutum 10, su ake bai wa man a Nijeriya gaba daya. Kuma a jihohin Adamawa da Taraba kwai muna da dillalan mai da suka kai dubu guda, balle a ce gaba daya Nijeriya.

Idan ka yi lissafi a Nijeriya muna da dillalan man fetur da suka haura dubu 30 da gudanar da harkokin mai. Amma a cikin bai wuce mutum 10 ake ba su mai ba, sannan a zo a ce ana ba mu mai, mu ba a ba mu mai ba, idan an ba mu kuma a fid da sunayenmu da yawan man da aka ba mu.

Wannan yanayin da ‘yan Nijeriya ke ciki a yanzu, ka ce an yi karin kudin mai a boye, ta yaya za ku fuskanci ‘yan Nijeriya?

To, ni kam na san yanda muka fuskanci wahala ne zai karu a kan wahala, yanzu ma muna sayen shinkafa dubu 35 a kan buhu guda, ko da yake NNPC sun ce za su ci gashin kansu ta yadda za su kawo kaya su sayar wa wadanda suke bukata.

Ina tabbatar wa gwamnati da ‘yan Nijeriya cewa, idan gwamnati ta ga cewa man nan ba za ta iya kawowa ba, ta tsamu hannunta ta mayar mana da shi tare da sayar mana da dala a farashi mai rahusa duk inda mai yake za mu iya kawowa har ya wadaci talakawan Nijeriya.

Wato dai kana jin ku za ku iya wadatar da ‘yan Nijeriya da mai tun da gwamnati ta gaza?

Wallahi za mu iya wadatarwa idan gwamnati ta ba mu izini, ta ba mu lasisi kamar yadda ta ba mu muka gina gidan mai. Idan gwamnati ta zabi wadanda za su iya ta ba su lasisi, wallahi za mu kawo mai da zai wadatar da Nijeriya, kuma shi zai kawo karshen matsalar man in Allah ya yarda.

Wani tabbaci kake da shi cewa idan kuka samu laisisin ba za a samu wata matsala ko karancin man ba?

Shi dan kasuwa a ko da yaushe dan kasuwa ne, wannan kuma shi ne kasuwancinmu, a cikinmu akwai mai gidajen mai 10, akwai mai gidan mai 20 a kwai mai 5, akwai mai gidan mai 1, gidan mai kuma idan ka gina ba ka sayar da mai ya zama kan go, to mene ne zai hana mu sayo wadataccen man. Wannan shi ne mafita a kan matsalolin man da muka tsinci kanmu a ciki.

Me kuke son ‘yan Nijeriya su fahimta game da ayyukanku?

Yauwa, al’ummar Nijeriya ina son su fahimci cewa matsalar mai ba daga wajanmu ba ne, yana hannun NNPC ne.

Matsalar rashin biya a shannun PEUM yake, DPR ba su da damuwa da mu. Mutum daya yake shugabantar hukumomin DPR, PPR da PEUM, amma ina tabbatar maka daga lokacin aka hada su a wuri daya zuwa yau ba mu gane mene muke a harkar man ba, domin babu wanda zai ce maka yau an biya shi kudinsa ban da mutanen da na kirga makannan.

Wannan kasuwancin na bukatar a sake dubawa, idan har gwamnati za ta biya mu hakkinmu, to komin zai daidaita, kuma in sha Allahu idan an yi haka kowa zai gani a kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AA RanoGwamnatin TarayyaIKMANKarancin MaiMan feturNNPCShugaban KungiyaYarjejeniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi

Next Post

Muhimmanci Koya Ma ‘Ya’ya Sana’oi Tun Suna kanana

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Muhimmanci Koya Ma ‘Ya’ya Sana’oi Tun Suna kanana

Muhimmanci Koya Ma ‘Ya’ya Sana’oi Tun Suna kanana

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.