Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da rufe dukkan makarantun firamare da sakandare a fadin jihar domin hutu na bikin Sallar Layya daga 4 zuwa 15 da 16 ga Yuni, 2025. Wannan sanarwa ta fito ne daga Daraktan wayar da kai na ma’aikatar Ilimi, Balarabe Kiru.
Sanarwar ta buƙaci iyaye da masu kula da ɗalibai a makarantun kwana da su kwashe ‘ya’yansu tun daga safiyar Laraba 4 ga Yuni, tare da tabbacin dawowa ranar Lahadi 15 ga Yuni, 2025.
- ‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
- Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Kiru ya bayyana cewa sauran sassan jadawalin karatun shekarar 2024/2025 da hutu na gwamnati da aka tsara a baya suna nan daram ba tare da sauyi ba.
Ya kuma nuna godiya ga haɗin kan iyaye da al’ummar jihar tare da kira da su tabbatar ‘ya’yansu sun koma makaranta a lokacin da aka tsara. Ya ce: “Muna yi wa ɗalibai da malamai fatan hutun Sallah mai albarka.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp