• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Koka Kan Yawaitar Satar Magani A Asibiti

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Gwamnatin Kano Ta Koka Kan Yawaitar Satar Magani A Asibiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta nuna damuwa game da yawaitar sata a cikin shirin bayar da magunguna kyauta, tana zargin wasu ma’aikatan lafiya da masu cin gajiyar shirin suna haɗa baki don satar magungunan da aka samar domin masu ƙaramin ƙarfi.

Kwamishinan Lafiya, Dr. Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da cibiyar hulɗa da Jama’a (CCSI) ta shirya, yana mai cewa wannan matsala tana kawo cikas ga nasarar shirin.

  • Kawu Sumaila Ya Yi Barazanar Maka Shugaban NNPP Na Kano A Kotu
  • An Jinjinawa Kokarin Sin Na Tallafawa Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Kasashen Afirka

Don magance matsalar, gwamnati ta fara amfani da tsarin rubutun bayanai na zamani da rajistar amfani domin tabbatar da gaskiya da adalci. Dr. Yusuf ya ce,

“Za a rubuta sunan, adireshi, da lambar waya na kowane mutum da ya karɓi waɗannan kayan, domin mu tabbatar da cewa an kai wa wadanda suka cancanta.”

Ya kuma koka kan rashin zuwa asibiti don kula da lafiya kafin haihuwa da bayan haihuwa a tsakanin mata, musamman a karkara, yana mai cewa hakan yana kara yawan mace-macen mata masu juna biyu.

Ya kara da cewa Gwamnatin Kano ta kammala wani bincike na shekara guda domin tattara bayanai kan mace-macen mata masu ciki a karkara, domin tsara matakan da za a ɗauka nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Har ila yau, an fara gyaran cibiyoyin lafiya da ɗaukar karin ma’aikatan lafiya don samar da ingantattun wuraren haihuwa cikin aminci ga mata masu ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoLafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

Next Post

Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki

Related

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
Kiwon Lafiya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

5 days ago
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
Kiwon Lafiya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
Kiwon Lafiya

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

3 weeks ago
Kwanciyar Aure
Kiwon Lafiya

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

4 weeks ago
Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi
Kiwon Lafiya

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

1 month ago
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
Kiwon Lafiya

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

2 months ago
Next Post
Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki

Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.