• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

by Abubakar Sulaiman
1 day ago
Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa raguwar farashin abinci da ake gani a kasuwanni a halin yanzu ya samo asali ne daga ƙaruwar samar da amfanin gona a cikin gida, da fito da kayan da  wasu suka boye, da kuma kyakkyawan haɗin gwuiwa tsakanin matakan gwamnatin tarayya da jihohi wajen daidaita isar da kayayyaki.

Ministan harkokin noma da tsaron Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na bikin Ranar Abinci ta Duniya ta shekarar 2025 a Abuja. Ya ce tsare-tsaren noma da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta aiwatar sun fara haifar da gagarumar nasara, inda manoma ke samun ƙarin amfanin gona daga muhimman kayayyakin abinci kamar shinkafa, da gero, da dawa, da rogo, da masara, da wake.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Abdullahi ya bayyana cewa rahoton binciken aikin noma na lokacin damina na 2025 da cibiyar NAERLS ta gudanar ya tabbatar da samun ci gaba a fannin noma. Ya ce hakan sakamakon ƙarin jarin da gwamnati ke zuba wa ne ta hanyar tallafin kayan noma, da rancen kudi, da shirin injinan noman zamani wanda ya rage wahalar manoma kuma ya ƙara yawan amfanin gona da ake samu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ta bayan da fifiko ga tsaron abinci, ba kawai wajen samarwa ba har ma wajen tabbatar da cewa talakawa na iya saya. Abdullahi ya ce yanke shawarar gwamnati na neman shigo da ɗan ƙaramin adadin abinci a bara ya sa masu boye kaya suka saki nasu saboda tsoron asara, wanda hakan ya ƙara yawan kayayyaki a kasuwa kuma ya sa dole a rage farashi.

A cewarsa, gwamnatocin jihohi suma suna taka rawa wajen kafa manyan rumfunan ajiya don daidaita farashi, musamman a jihohin Kaduna, da Kano, da Jigawa da Neja. Ya ce gwamnatin tarayya tana ci gaba da tallafawa manoma ta hanyar bayar da kayan noma kyauta da sauƙaƙa musu samun injinan noma domin rage kuɗin samarwa da ƙarfafa ci gaba da noman zamani.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Next Post
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.