• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa raguwar farashin abinci da ake gani a kasuwanni a halin yanzu ya samo asali ne daga ƙaruwar samar da amfanin gona a cikin gida, da fito da kayan da  wasu suka boye, da kuma kyakkyawan haɗin gwuiwa tsakanin matakan gwamnatin tarayya da jihohi wajen daidaita isar da kayayyaki.

Ministan harkokin noma da tsaron Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na bikin Ranar Abinci ta Duniya ta shekarar 2025 a Abuja. Ya ce tsare-tsaren noma da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta aiwatar sun fara haifar da gagarumar nasara, inda manoma ke samun ƙarin amfanin gona daga muhimman kayayyakin abinci kamar shinkafa, da gero, da dawa, da rogo, da masara, da wake.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Abdullahi ya bayyana cewa rahoton binciken aikin noma na lokacin damina na 2025 da cibiyar NAERLS ta gudanar ya tabbatar da samun ci gaba a fannin noma. Ya ce hakan sakamakon ƙarin jarin da gwamnati ke zuba wa ne ta hanyar tallafin kayan noma, da rancen kudi, da shirin injinan noman zamani wanda ya rage wahalar manoma kuma ya ƙara yawan amfanin gona da ake samu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ta bayan da fifiko ga tsaron abinci, ba kawai wajen samarwa ba har ma wajen tabbatar da cewa talakawa na iya saya. Abdullahi ya ce yanke shawarar gwamnati na neman shigo da ɗan ƙaramin adadin abinci a bara ya sa masu boye kaya suka saki nasu saboda tsoron asara, wanda hakan ya ƙara yawan kayayyaki a kasuwa kuma ya sa dole a rage farashi.

A cewarsa, gwamnatocin jihohi suma suna taka rawa wajen kafa manyan rumfunan ajiya don daidaita farashi, musamman a jihohin Kaduna, da Kano, da Jigawa da Neja. Ya ce gwamnatin tarayya tana ci gaba da tallafawa manoma ta hanyar bayar da kayan noma kyauta da sauƙaƙa musu samun injinan noma domin rage kuɗin samarwa da ƙarfafa ci gaba da noman zamani.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.