ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Yadda Dalibai Za Su Samu Bashi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Dalibai

Gwamnatin tarayya ta bayyana yadda dalibai za su samu bashi karkashin shirin da ta bullo da shi domin tallafa musu wajen gudanar da karatunsu cikin sauki.

A cewar gwamnatin tarayya, shirin zai gudana ne a zamance ba sai daliban sun sha wata wahala wajen samun wannan bashi ba.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024

Babban sakataren shirin bai wa dalibai bashi na kasa, Dakta Akintunde Sawyerr shi ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa jim kadan bayan sun kammala ganawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana masa cewa an samu nasarar taura kudaden bai wa dalibai bashi a asusun makarantu.

ADVERTISEMENT

Shirin zai kuma bai wa matasan Nijeriya daman samun horon sana’o’I bayan kammala makarantun gaba da sakandare.

Sawyerr ya yi wannan bayani ne ga manema labarai tare da shugaban hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS), Dakta Zacch Adedeji.

LABARAI MASU NASABA

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Shi me Dakta Adedeji ya tofa albarkacin bakinsa, inda ya bayyana cewa sun gana da shugaban kasa ne saboda harajin ilimi shi ne babban hanyar samun kudin da za a bai wa dalibai bashi.

Sawyerr ya kara da cewa shirin zai taimaka wa dalibai wajen bangaren sana’ar da suke burin cimmawa, maimakon tilasta musu kan wani lamari saboda karancin kudade wajen gudanar da harkokin karatu.

Ya tabbatar da cewa shirin zai taimaka matuka gaya na hatsarin da matasan Nijeriya ke fadawa lokacin da suke yunkurin shiga kasashen Turai domin samun rayuwa mai inganci.

Sawyerr ya ce, “Mun yi tunani sosai kafin fara wannan shirin. Idan har dalibai ya bukaci wannan bashi, to ba sai ya hadu da wani mutum ba. Akwai manhaja da dalibi zai shiga wajen neman bashin.

“Ko wani dalibi da ke sha’awar amsar bashin kwai zai shiga manhajan ne sai ya cika abubuwan da ake bukata domin samun cikakken bayaninsa. Abubuwan da ake bukata sun hada da lambar jarrabawar shiga manyan makaranta da bangaren da yake karatu da kuma ranar haihuwa.

“Sauran sun hada da lambar dan kasa wanda zai tabbatar da cewa shi dan Nijeriya ne, domin bashin ana bai wa daliban Nijeriya ne kadai. Katin dan kasa zai taimaka mana wajen bayyana sahihancin bayanan dalibi. Sannan ana bukatar lambar BBN, wannan zai taimaka wajen sanin asusun dalibi.

“An kirkiri wannan shirin ne domin tallafa wa daliban Nijeriya wadanda ba za su iya biyan kudin makaranta ba, sannan kuma zai taimaka musu wajen samun sana’oin dogaro da kai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya
Ilimi

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.