• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Yadda Dalibai Za Su Samu Bashi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Ilimi
0
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana yadda dalibai za su samu bashi karkashin shirin da ta bullo da shi domin tallafa musu wajen gudanar da karatunsu cikin sauki.

A cewar gwamnatin tarayya, shirin zai gudana ne a zamance ba sai daliban sun sha wata wahala wajen samun wannan bashi ba.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024

Babban sakataren shirin bai wa dalibai bashi na kasa, Dakta Akintunde Sawyerr shi ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa jim kadan bayan sun kammala ganawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana masa cewa an samu nasarar taura kudaden bai wa dalibai bashi a asusun makarantu.

Shirin zai kuma bai wa matasan Nijeriya daman samun horon sana’o’I bayan kammala makarantun gaba da sakandare.

Sawyerr ya yi wannan bayani ne ga manema labarai tare da shugaban hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS), Dakta Zacch Adedeji.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Shi me Dakta Adedeji ya tofa albarkacin bakinsa, inda ya bayyana cewa sun gana da shugaban kasa ne saboda harajin ilimi shi ne babban hanyar samun kudin da za a bai wa dalibai bashi.

Sawyerr ya kara da cewa shirin zai taimaka wa dalibai wajen bangaren sana’ar da suke burin cimmawa, maimakon tilasta musu kan wani lamari saboda karancin kudade wajen gudanar da harkokin karatu.

Ya tabbatar da cewa shirin zai taimaka matuka gaya na hatsarin da matasan Nijeriya ke fadawa lokacin da suke yunkurin shiga kasashen Turai domin samun rayuwa mai inganci.

Sawyerr ya ce, “Mun yi tunani sosai kafin fara wannan shirin. Idan har dalibai ya bukaci wannan bashi, to ba sai ya hadu da wani mutum ba. Akwai manhaja da dalibi zai shiga wajen neman bashin.

“Ko wani dalibi da ke sha’awar amsar bashin kwai zai shiga manhajan ne sai ya cika abubuwan da ake bukata domin samun cikakken bayaninsa. Abubuwan da ake bukata sun hada da lambar jarrabawar shiga manyan makaranta da bangaren da yake karatu da kuma ranar haihuwa.

“Sauran sun hada da lambar dan kasa wanda zai tabbatar da cewa shi dan Nijeriya ne, domin bashin ana bai wa daliban Nijeriya ne kadai. Katin dan kasa zai taimaka mana wajen bayyana sahihancin bayanan dalibi. Sannan ana bukatar lambar BBN, wannan zai taimaka wajen sanin asusun dalibi.

“An kirkiri wannan shirin ne domin tallafa wa daliban Nijeriya wadanda ba za su iya biyan kudin makaranta ba, sannan kuma zai taimaka musu wajen samun sana’oin dogaro da kai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Next Post

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Related

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

2 weeks ago
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Ilimi

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

2 weeks ago
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje
Ilimi

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
Ilimi

Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)

4 weeks ago
Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
Labarai

Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano

4 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Ranar Australia Ga Gwamna Janar Na Kasar

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.