• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Jinjina Wa Kamfanin BUA Bisa Karya Farashin Buhun Siminti Zuwa Naira 3,500

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Jinjina Wa Kamfanin BUA Bisa Karya Farashin Buhun Siminti Zuwa Naira 3,500
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta jinjina wa kamfanin siminti na BUA bisa karya farashin buhun siminti daga naira 5,500 zuwa 3,500.

Da yake yaba wa kamfanin, ministan gidaje da raya birane, Ahmed Musa Dangiwa, ya bayyana cewa wannan shiri da aka yi zai rage tsadar siminti, wanda ke da tsada wajen gina gidaje.

  • Huldar Banki Da Babu Ruwa: Bankin TAJ Ya Samu Ribar Naira Biliyan 6 A Zangon Farko
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

A cewarsa, zai goyi bayan ajandar Shugaba Kasa Bola Tinubu na samar da gidaje masu sauki ga ‘yan Nijeriya.

Ministan ya bayyana haka ne a matsayin martani ga sanarwar da kamfanin BUA ya bayar a ranar 1 ga Oktoba, 2023 a hukumance ta rage farashin siminti a Nijeriya.

Ya kara da cewa tsadar siminti ya haifar da tashin gwauron zabi na gidaje, wanda hakan ya sa talakawan Nijeriya ba za su iya biya ba. Ministan ya kara da cewa matakin na kamfanin BUA wani gagarumin ci gaba na saukaka kudi a kan masu neman gida.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Dangiwa ya jaddada cewa tun da ya hau kujerar  minista, ya fara inganta samar da gidaje masu saukin kudi a matsayin babban abin da ya bai wa fifiko bisa tsarin ajandar shugaban kasa.

“Tashin farashin kayayyakin gine-gine, musamman siminti, ya kawo cikas ga ‘yan Nijeriya masu bukatar mallakar gidaje. Matakin da kamfanin BUA ya dauka na rage farashin siminti zuwa naira 3,500 abin yabawa ne matuka. Ya nuna fahimtar gwagwarmayar da talakawan Nijeriya ke fuskanta kuma mataki ne mai kyau na samar da gidaje mafi araha da kowa ke bukata.

“Na yaba wa kamfanin BUA saboda shawarar da ya yanke na rage farashin siminti. Matsuguni masu araha hakki ne na asali kuma wannan matakin ba shakka zai rage kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta. Yana nuna sadaukarwar da aka yi na inganta rayuwar al’ummarmu da kuma cimma muradin bukasa burane,” in ji shi.

Dangiwa ya bukaci sauran kamfanoni su yi koyi da BUA, inda ya bukace su da su yi la’akari da tasirin yadda wannan mataki zai bukasa rayuwar al’umma.

Ya bayyana kokarin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu wajen magance matsaloli rashin mallakar muhalli ga dukkan ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Bayar Da Mafita Kan Yadda Za A Samu Zaman Lafiya A Duniya

Next Post

Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

2 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

4 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

7 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

9 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

10 hours ago
Next Post
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)

LABARAI MASU NASABA

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.