• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Jinjina Wa Kamfanin BUA Bisa Karya Farashin Buhun Siminti Zuwa Naira 3,500

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
BUA

Gwamnatin tarayya ta jinjina wa kamfanin siminti na BUA bisa karya farashin buhun siminti daga naira 5,500 zuwa 3,500.

Da yake yaba wa kamfanin, ministan gidaje da raya birane, Ahmed Musa Dangiwa, ya bayyana cewa wannan shiri da aka yi zai rage tsadar siminti, wanda ke da tsada wajen gina gidaje.

  • Huldar Banki Da Babu Ruwa: Bankin TAJ Ya Samu Ribar Naira Biliyan 6 A Zangon Farko
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

A cewarsa, zai goyi bayan ajandar Shugaba Kasa Bola Tinubu na samar da gidaje masu sauki ga ‘yan Nijeriya.

Ministan ya bayyana haka ne a matsayin martani ga sanarwar da kamfanin BUA ya bayar a ranar 1 ga Oktoba, 2023 a hukumance ta rage farashin siminti a Nijeriya.

Ya kara da cewa tsadar siminti ya haifar da tashin gwauron zabi na gidaje, wanda hakan ya sa talakawan Nijeriya ba za su iya biya ba. Ministan ya kara da cewa matakin na kamfanin BUA wani gagarumin ci gaba na saukaka kudi a kan masu neman gida.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Dangiwa ya jaddada cewa tun da ya hau kujerar  minista, ya fara inganta samar da gidaje masu saukin kudi a matsayin babban abin da ya bai wa fifiko bisa tsarin ajandar shugaban kasa.

“Tashin farashin kayayyakin gine-gine, musamman siminti, ya kawo cikas ga ‘yan Nijeriya masu bukatar mallakar gidaje. Matakin da kamfanin BUA ya dauka na rage farashin siminti zuwa naira 3,500 abin yabawa ne matuka. Ya nuna fahimtar gwagwarmayar da talakawan Nijeriya ke fuskanta kuma mataki ne mai kyau na samar da gidaje mafi araha da kowa ke bukata.

“Na yaba wa kamfanin BUA saboda shawarar da ya yanke na rage farashin siminti. Matsuguni masu araha hakki ne na asali kuma wannan matakin ba shakka zai rage kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta. Yana nuna sadaukarwar da aka yi na inganta rayuwar al’ummarmu da kuma cimma muradin bukasa burane,” in ji shi.

Dangiwa ya bukaci sauran kamfanoni su yi koyi da BUA, inda ya bukace su da su yi la’akari da tasirin yadda wannan mataki zai bukasa rayuwar al’umma.

Ya bayyana kokarin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu wajen magance matsaloli rashin mallakar muhalli ga dukkan ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.