• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Albarkatun Ruwa, Farfesa Joseph Terlumun Utseb, ya kaddamar da shirin noman rani; wanda aka yi wa lakabi da ‘Rafin-Yashi’.

Haka zalika, shirin ya kunshi samar da kadadar noma sama da guda 28 da kuma  gonar Songhai da ke karkashin hukumar kula da kogin Neja, domin kara habaka noman rani tare da lalubo  mafita a kan karancin abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

  • NPA Ta Gargadi Masu Jibge Kwantaina Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Dawo Da Ma’aikatan Da Ta Dakatar Da Ganduje Ya Ɗauka Aiki

Sannan Minsitan, ya kaddamar da tankunan ruwa sama da 700,000, wadanda za a iya adanawa tare da yin tanadin ruwa domin yin noman rani.

A cewar tasa, “daya daga cikin tankunan ruwan; za su rika yin amfani da shi wajen tura ruwa zuwa Rafin-Yashi, domin aiwatar da noman rani, inda sauran kuma za a rika amfani da su wajen tura ruwa zuwa gonar Songhai.

Har ila yau, Dam din Rafin Yashi, wanda guda ne cikin ayyukan da ministan ya kaddamar, ya kai zurfin kimanin kafa 650,000, wanda ko shakka babu zai yi matukar taimakawa; wajen rage ambaliyar ruwan sama a tsakanin al’ummar da ke zaune kusa da Dam din na Rafin Yashi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

Ministan ya kara da cewa, idan aka kammala aikin wannan Dam, zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da noman rani tare da taimakawa wajen kirkiro da ayyuakan yi da farfado da tattalin arzikin wannan kasa da kuma habaka samar da wadataccen abin abinci, wanda hakan ya yi daidai da kudire-kudiren Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Bugu da kari, ya sanar da cewa, a makon da ya gabata; ma’aikatarsa ta kaddamar da ayyukan noman rani na shekarar 2023, domin bunkasa samar da wadataccen abinci  a fadin kasar.

Ministan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja, ta samar da wadatacciyar kasa a Hukumar Kula da Kogin Neja, domin a rika yin noman rani, don amfanin jihar da kuma kasa baki-daya

Kazalika, ya sanar da cewa; akwai bukatar Gwamnatin Jihar ta samar da kayan aikin noman rani tare da bai wa ‘yan jihar kwarin guiwar rungumar yin ayyukan na noman rani, a cewar tasa wannan hanyar ce kadai za a kara samar da wadataccen abinci a fadin dukkanin wannan kasa.

Har wa yau ya kara da cewa, dole ne a samar da wadataccen abinci ga kafatanin ‘yan Nijeriya da kuma wanda za a rika fitarwa zuwa kasashen ketare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Bukaci Japan Ta Amince Kasashen Duniya Su Sa Ido Kan Yadda Take Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Next Post

Yadda Ake Hada Turaren Hammata

Related

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

5 minutes ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 weeks ago
Next Post
Yadda Ake Hada Turaren Hammata

Yadda Ake Hada Turaren Hammata

LABARAI MASU NASABA

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.