• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Karbe Filin Jirgin Saman Gombe

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Karbe Filin Jirgin Saman Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

Gwamnatin Tarayya ta bada izinin kwace ikon gudanar da Filin Jirgin Sama na Jihar Gombe.

Gwamna Inuwa Yahaya na jihar ne ya sanar da hakan a Fadar Shugaban Kasa, yana mai cewa matakin zai bayu ga samar da karin kayan aiki da kudaden gudanarwa gami da ingantuwar aiki a filin jirgin.

  • Manyan ‘Yan Majalisar Birtaniya Sun Yi Mubaya’a Ga Sabon Sarki, Charles
  • An Tattauna Kan Wasu Daftarorin Da Za A Yi Nazarinsu Yayin Zaman Kwamitin Kolin JKS
Gwamnan ya bayyana a ranar Juma’a cewa, “Mafi mahimmanci shi ne komawan Filin Jirgin Sama na Gombe hannun Gwamnatin Tarayya da Shugaba Buhari ya amince.“Tuni Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta fara gina barikinta a hafabar filin jirgin , wanda iya ya koma hannun Gwamnatin Tarayya zai samu karin kayan aiki da na gudanarwa, musamman tunda filayen jiragen sama na cikin jerin ayyuka na musamman a karkashin doka.

“Hakan na nufin za a samu karin kayan aiki da gudanarwa mai inganci kuma za a fada shi ta yadda ayyukan tattalin arziki za su habaka saboda samuwar filin jirgin, wanda zai taimaka wajen bunkasa harkokin kasuwanci.”

A watan Yuni ne Hukumar Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAAA) ta gudanar da bincike kan kayan aikin Filin Jiragen Sama na Gombe, har ta sahale masa izinin jigilar maniyyata aikin Hajji zuwa kasar Saudiyya.

Game da ziyararsa Fadar Shugaban Kasa, Gwamna Inuwa Yahaya ya ce ya je ne domin yin godiya bisa muhimman ayyukan ci gaba da Gwamnatin Tarayya ta yi a Jihar Gombe.

Ya ce ayyukan za su bunkasa harkokin tattalin arzikin da samar da ayyukan yi tare da dakile ayyukan ’yan ta’adda da rahotanni suka tabbatar cewa sun fara taruwa a yankin Gandun Dajin Wawa-Zange da ke jihar.

Ya ce manyan ayyukan saun hada da na gyaran babbar titin Gombe zuwa Bauchi, wanda shi ne ya dangana har zuwa Yobe har zuwa Maiduguri.

Sauran ayyukan sun hada da na fadada aikin samar da ruwa na Gombe, wanda ya ce shi ne babbar hanyar samar da ruwa ga garin Gombe da yankunan da ke makwabtaka da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin Saman GombeGwamnatin TarayyaIkoShugaba Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ta Watsa Shagalin Murnar Bikin Tsakar Yanayin Kaka Ta Shekarar 2022

Next Post

Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta – Hauwa Yusuf

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

2 hours ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

6 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

7 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

8 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

9 hours ago
Next Post
Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta – Hauwa Yusuf

Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta - Hauwa Yusuf

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.