ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Karbe Filin Jirgin Saman Gombe

by Sadiq
4 years ago
Gombe

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

ADVERTISEMENT

Gwamnatin Tarayya ta bada izinin kwace ikon gudanar da Filin Jirgin Sama na Jihar Gombe.

Gwamna Inuwa Yahaya na jihar ne ya sanar da hakan a Fadar Shugaban Kasa, yana mai cewa matakin zai bayu ga samar da karin kayan aiki da kudaden gudanarwa gami da ingantuwar aiki a filin jirgin.

  • Manyan ‘Yan Majalisar Birtaniya Sun Yi Mubaya’a Ga Sabon Sarki, Charles
  • An Tattauna Kan Wasu Daftarorin Da Za A Yi Nazarinsu Yayin Zaman Kwamitin Kolin JKS
Gwamnan ya bayyana a ranar Juma’a cewa, “Mafi mahimmanci shi ne komawan Filin Jirgin Sama na Gombe hannun Gwamnatin Tarayya da Shugaba Buhari ya amince.“Tuni Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta fara gina barikinta a hafabar filin jirgin , wanda iya ya koma hannun Gwamnatin Tarayya zai samu karin kayan aiki da na gudanarwa, musamman tunda filayen jiragen sama na cikin jerin ayyuka na musamman a karkashin doka.

“Hakan na nufin za a samu karin kayan aiki da gudanarwa mai inganci kuma za a fada shi ta yadda ayyukan tattalin arziki za su habaka saboda samuwar filin jirgin, wanda zai taimaka wajen bunkasa harkokin kasuwanci.”

A watan Yuni ne Hukumar Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAAA) ta gudanar da bincike kan kayan aikin Filin Jiragen Sama na Gombe, har ta sahale masa izinin jigilar maniyyata aikin Hajji zuwa kasar Saudiyya.

Game da ziyararsa Fadar Shugaban Kasa, Gwamna Inuwa Yahaya ya ce ya je ne domin yin godiya bisa muhimman ayyukan ci gaba da Gwamnatin Tarayya ta yi a Jihar Gombe.

Ya ce ayyukan za su bunkasa harkokin tattalin arzikin da samar da ayyukan yi tare da dakile ayyukan ’yan ta’adda da rahotanni suka tabbatar cewa sun fara taruwa a yankin Gandun Dajin Wawa-Zange da ke jihar.

Ya ce manyan ayyukan saun hada da na gyaran babbar titin Gombe zuwa Bauchi, wanda shi ne ya dangana har zuwa Yobe har zuwa Maiduguri.

Sauran ayyukan sun hada da na fadada aikin samar da ruwa na Gombe, wanda ya ce shi ne babbar hanyar samar da ruwa ga garin Gombe da yankunan da ke makwabtaka da shi.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta – Hauwa Yusuf

Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta - Hauwa Yusuf

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.