ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Fara Karatun Digiri Da Yaren Tibi Da Nupe A Jami’o’i

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 weeks ago
NUC

Hukumar Kula da Jami’o’in Kasa (NUC) ta kaddamar da yunkurin gabatar da harsunan Tib da Nupe a matsayin manhajojin karatu a jami’o’in Nijeriya.

Wannan yunkuri, da Sakataren Zartarwa na NUC, Farfesa Abdullahi Ribadu, ke jagoranta, na nufin sanya wadannan harsuna a matsayin darussa na digirin farko, wanda zai zama babban mataki wajen amincewa da kuma adana gadon harsunan Nijeriya.

  • NDLEA Ta Cafke Mutane 230 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho

A matsayin wani bangare na wannan tsari, an dauki kwararru daga jami’o’in Nijeriya domin tsara Ka’idojin Mafi Karancin Darussan Asali (CCMAS) don sabbin shirye-shiryen.

ADVERTISEMENT

Wannan mataki ya sanya harsunan Tib da Nupe a matsayin sabbin kari a cikin jerin harsunan da ake koyarwa a jami’o’in Nijeriya.

A da ana koyon wadannan harsuna ne a matsayin darussa na zabi ko batutuwan bincike, amma yanzu za a samar da cikakkun shirye-shiryen digiri da aka tsara domin samar da dalibai masu ilimi mai zurfi a fannin harshe, adabi, da al’adun zamantakewa.

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Shirye-shiryen kuma suna da nufin karfafa adana al’adu da kuma yaki da barazanar bacewar harsuna.

A cewar bayanan NUC, manyan masu ba da shawarwari don shirye-shiryen su ne Farfesoshi Mary Adebayo (Tib) da Rebecca K. D. (Nupe).

Masu tallafawa ci gaban darussan sun hada da Farfesoshi Muhammad Alkali da Musa Bawa don Tib, da Farfesoshi John Akosu Adeiyongo da Nguton Sambe don Nupe.

Kwamitin kuma ya hada da wakilan NUC: Florence Onuoha, Chinenye Augustine, Kate Omotayo Onaiyekan, da Hadiza Kalla.

Idan za a iya tunawa an gudanar da wani taron bita na kwanaki hudu a Hedikwatar NUC daga 21 zuwa 24 ga Oktoba, 2025, inda aka hada kwararrun masu ruwa da tsaki don shirya tsarin CCMAS.

Wannan yunkuri ya biyo bayan damuwa kan rauni da kuma barazanar da harsunan gida fiye da 500 na Nijeriya ke fuskanta, da dama daga cikinsu suna karkashin inuwa ta harshen Turanci da manyan harsunan gida kamar Hausa, Yoruba, da Igbo.

Harsunan Tib, da ake magana da shi sosai a Jihar Benue da kewaye, da Nupe, wanda ya yi fice a jihohin Niger, Kogi, da Kwara, yanzu za su samu dandamali na ilimi da aka tsara, wanda zai shirya dalibai don koyarwa, bincike, da habaka wadannan harsuna a makarantu, kafofin yada labarai, da cibiyoyin al’adu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Riyadh 2025: Nijeriya Ta Zo Matsayi Na 8 Da Lambobin Yabo 30

Riyadh 2025: Nijeriya Ta Zo Matsayi Na 8 Da Lambobin Yabo 30

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.