ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho

by Sulaiman and Bello Hamza
7 months ago
ruwa

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta jaddada mahimmancin hadaka da dagaro a tsakanin kasasehn da ke Afirka, domin a kara karfafa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a daukacin nahiyar

Shugaban Hukumar Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana haka a cikin sanawar da ya fitar a ranar Lahadi, yayin rufe taron karo na 45 na shekara-shekara na Kungiyar Masu Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Afirka ta Yamma wato PMAWCA da aka kammla a yankin Pointe-Noire na Jamhuriyar Kongo.

  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki
  • Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba

Dantsoho wanda kuma shi ne, Shugaban kungiyar, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda aka gudanar da tattaunawa a taron da kuma sakwanin fatan alheri da aka gabatar a taron wanda ya sanar da cewa, hakan ya nuna cewa, kasashen da ke ba cikin kungiyar, a shirye suke, domin ganin an kawo karshen kalubalen da fannin ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Shugaban wanda Janar Manaja na sashen hulda da Jama’a a Hukumar Ikechukwu Onyemekara ya wakilce shi a wajen rufe taron, inda ya sanar da cewa, matsayar da aka cimma a wajen taron, za a yi amfani da su, wajen samar da tsare-tsare da karfafa yuinkurin matakan gwamnati da ke a cikin kasashen da ke a yankin na Afirka ta Yamma.

“A madadin mu da ke a wannan kungiyar ta PMAWCA, muna godiya da lokacinku da kuka bayar da kuma irin kwarewar da ku bayar domin kara habaka hada-hadar kasuwanci da kokarin da ku ka yi, domin amfana da albakatun da ke a bangaren tafiyar da harkar sufurin Jiragen Ruwa a yankin, “ Inji Dantsoho.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

“Duba da irin sakonnin da kuka gabatar a wajen taron, musamman a zaman taron na musamman hakan ya nuna cewa, a shirye kuke wajen kara kwarin Guiwar fannin na sufurin Jiragen Ruwa da ke a yankin, “ A cewar Shugaban.

A cewarsa, yanayin tasawirar kasa da kuma tattalin arzkin da ke a yankin a zahirance, hakan ya nuna bukatar karfafa hadin kai, musamman domin a kara bunkasa fannin wajen samar da kyakyawan yanayi, tamkar na fadin duniya.

Dantsoho ya kuma nuna jin dadinsa ga Gwamnati da daukacin alummar Jamhiriyar ta Kongo kan karbar bakuncin taron tare da yabawa Sakatare Janar na kungiyar ta PMAWCA, Mista Koffi Jean Marie da kuma tawagar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Pointe-Noire da sauran abokan hadaka.

Kazalika, ya yaba da kokarin da Darakta Janar na He further da kuma Babban Shugaba da sauran mambobi na Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a yankin kan gudunmawar da suka bayar.

Dantsoho ya kuma bukaci da a ci gaba da yin hadaka, domin a kara ciyar da fannib gaba.

An kirkiro da kungiyar ta PMAWCA a watan Okutobar shekarar 1972 a karkashin Hukumar kula da tattalin arziki na Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin Freetown, na kasar Sierra Leone.

Kungiyar ta kunshi Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma wadda kuma ta yadu, zuwa kasar Mauritania, har zuwa kasar Angola.

Kazalika,  babbar manufar kungiyar shi ne, kara karfafa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da kara samar da kayan aiki a tsakanin ‘ya’yan kungiyar da ke a yankin, musaman domin a bunkasa tattalin azrki da ke a yankin.

Aikin Sabunta Tashoshin Jiragen Ruwa Na Warri Da Koko Za Su Bunkasa Kasuwanci A Nijeriya—NPA

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta alakanta aikin sabunta Tashoshin Jiragen Ruwa na garin Warri da Koko, da ke a jihar Delta, a matsayin wani mataki, na kara gina kasar.

NPA ta kuma yi alkwarin mayar da hada-hadar kasuwanci a Tashoshin, zuwa na bai daya.

Hakan na kunshe ne, a cikin wani kundin tsari da Jaridar The Guardian ta samu.

Hukumar ta ce, aikin zai kasance, tamkar an bude wani sabon babi ne, na samar da damar a yankin.

A cewar NPA, manufar shi ne, domin a maganace cunkoson da ake samu a Tashoshin Jiragen Ruwa na jihar Legas, musamman duba da cewa, Tashoshin na jihar Delta yadda aka tsara su,  za su samar da sauki ga yankin Kudu Maso Kudu da Yankin Arewa ta Tsakiya

Baya ga kara habaka hjanyoyin Ruwa na jihar ta Delta zuwa samar da hanyoyin gudanar da hada-hadar kasuwanci aikin na sabuntawar, zai bai wa sauran alumomin damar amfana da aikin.

Wani bincike da Jaridar ta The Guardian ta gudanar, ya nuna yadda aikin sabuntawar zai kara bunkasa ayyukan NPA.

Bisa irin kayan aikin da NPA ke da su, sun nuna cewa, Jiragen Ruwa za su  iya sauke kayan da nauyinsu, ya kai tan 293,013 a Tashoshin na jihar Delta, wanda hakan ya kai kaso 10.7  a cikin dari, na yawan hada-hadar da a iya yi, a Tashoshin na Delta.

Ayyukan da NPA ke ci gaba da aiwatarwa abu ne a zahirance, ba wai tatsuniya ba.

Aikin yashe hanyoyin Ruwa na Escrabos da sabunta Tashoshin isar da sakon kota kwana da sanya kayan tsaro a SPB Likoro, wani abu ne, da ke nuna irin kwararran matakan da aka dauka domin karfafa gudanar da ayyuka.

Kazalika, Hukumar ta  NPA, ta kara jaddada bai wa masu son zuba hannun jari a fannin, kwarin Guiwa ta hanyar tabbatar da ana bin ka’ida da zauka matakan da suka kamata a Tashoshin na jihar Delta

ruwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
ruwa
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Nemi A Ɗauki Sabbin Ma’aikata A Jami’o’in Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi A Ɗauki Sabbin Ma’aikata A Jami’o’in Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.