• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago
Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ɗauki sababbin malamai 500 gwamnati, a wani yunƙuri na ci gaba da farfaɗo da sashin ilimi a faɗin jihar. Shugaban hukumar kula da aiyukan ma’aikata ta Jihar Zamfara kuma shugaban kwamitin ɗaukar ma’aikata, Aliyu Mohammed Tukur, ne ya bayyana haka, yana mai cewa tsarin ɗaukar aikin ya kasance mai tsauri da cancanta.

A cewarsa, mutane 11,708 ne suka nemi aikin koyarwa ta hanyar manhajar yanar gizo ta gwamnati, inda daga cikinsu 8,184 suka cika sharuɗɗan farko kuma aka tantance su. Daga cikin wannan adadi, mutane 3,105 ne suka shiga jarabawar kwamfuta (CBT), sannan 1,033 daga cikinsu suka samu shiga tantancewar baki da baki ta ƙarshe. Bayan nazari da kimantawa, mutane 500 aka zaɓa domin ɗauka a matsayin malamai a makarantun jihar.

Tukur ya ce sababbin malamai sun kware a fannoni masu muhimmanci kamar Turanci, Lissafi, Kimiyya, da kuma Koyon Sana’o’i (Vocational Studies). Ya kuma yabawa Ma’aikatar Ilimi, da Kimiyya da Fasaha bisa jajircewarta wajen tabbatar da nasarar tsarin ɗaukar aikin. “Wannan ɗaukar aiki babbar nasara ce wajen magance ƙarancin malamai da kuma inganta ingancin ilimi a makarantun gwamnati,” in ji Tukur.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta tura sababbin malamai zuwa makarantun da ke ko’ina cikin jihar, tare da bai wa yankunan karkara da waɗanda ba su da isassun malamai fifiko. Wannan mataki, a cewarsa, yana cikin shirin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa kowane yaro a Zamfara yana samun ingantaccen ilimi, ba tare da bambanci ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.