• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Maso Yamma Na Yunkurin Zamanantar Da Aikin Gona

by Abubakar Abba
2 years ago
Aikin Gona

Gwamnonin arewa maso yammacin Nijeriya sun garzaya Abidjan, domin halartar taron zamanantar da ayyukan gona da yadda ake sarrafawa ta hanyar masana’antu.

Gwamnonin su bakwai sun bar Nijeriya ne a ranar Laraba, 15 ga Nuwamba, wanda aka shirya za su gana da shugaban bankin raya Nahiyar Afirka, Dakta Akinwumi Adesina.

  • Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin
  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

A cikin sanarwar da mai magana da yawan gwamnan Jihar Zamfana, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce sun tafi Abidjan ne domin amfani da damar wajen duba shirin zamanantar da ayyukan noma.

Ya kara da cewa gwamnonin guda bakwai sun hada da na jihohin Zamfara, Sakkwato, Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano da kuma Kebbi.

“Gwamnonin yankin arewa maso yammacin Nijeriya za su gana da shugaban bankin bankasa nahiyar Afirka, Dakta Akinwumi Adesina da kuma tawagarsa.

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

“An shirya gudanar da taron ne a ranar 16 ga Nuwambar 2023, kuma zai hada da gabatar da bayanai kan zamanantar da ayyukan aikin gona.

“Shirin ya hada har da samar da masana’antu na musamman na noma ta yadda za a samu nasarar samar da wadataccen abinci, samar da ayyukan yi, bunkasa tattalin arziki ta hanyar sarraba amfanin gona a yankuna daban-daban.

“Mataimakiyar shugaban ayyukan noma na bankin bunkasa yankin Afirka, Dakta Beth Dunford za ta jagoranci gwamnoni kan yadda ake sarrafa amfanin gona ta hanyar masana’antu da kuma abubuwan da ya kamata gwamnonin su yi domin cin gajiyar shirin.

“Babban mashawarcin shugaban bankin raya Afirka kan masana’antu, Farfesa Oyebanji Oyelaran-Oyeyinka zai yi wa gwamnonin bayani kan irin mataki na daya da na biyu na shirin domin inganta shi a jihohinsu,” in ji Idris.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Yadda Za A Sake Farawa Daga Birnin San Francisco

Yadda Za A Sake Farawa Daga Birnin San Francisco

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.