ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

by CMG Hausa
3 years ago
People walk past APEC Summit signage displayed at Moscone North on Monday, Nov. 13, 2023, in San Francisco. (Lea Suzuki/San Francisco Chronicle via AP)

People walk past APEC Summit signage displayed at Moscone North on Monday, Nov. 13, 2023, in San Francisco. (Lea Suzuki/San Francisco Chronicle via AP)

A ranar Alhamis ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da rubutaccen jawabi ga taron jagororin masana’antu da kasuwanci na kungiyar hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik ko APEC a takaice, a birnin San Francisco na kasar Amurka.

Shugaba Xi ya ce shekaru 30 da suka gabata, jagororin yankin Asiya da Fasifik, bisa burin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba, sun gudanar da kwarya-kwaryar taro na farko na shugabannin APEC, da nufin ingiza ci gaba, da hade sassan tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik da na sauran sassan duniya, ta yadda hakan ya dora yankin kan turba ta gaggauta samun ci gaba, tare da taimakawa yankin wajen zama cibiyar bunkasar tattalin arzikin duniya.

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa,duniya ta shiga wani sabon lokaci na tangal tangal da sauye sauye, kana ina za a dosa wajen aiwatar da hadin gwiwar yankin Asiya da Pasifik nan da shekaru 30 masu zuwa, ta zama sabon batu dake jan hankali a wannan lokacin da muke ciki. Dole ne mu mara baya ga ainihin burin hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik ko APEC, kana mu ingiza sabon kuzari ga hadin gwiwar kungiyar.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ya zama wajibi mu hada karfi da karfe wajen tabbatar da nasarar manufofi, da ka’idojin dake kunshe cikin tsarin dokokin MDD, mu nacewa turbar tattaunawa ba tare da fito na fito ba, mu wanzar da ci gaba da daidaito a yankin Asiya da Fasifik. Bai dace ba, kuma yankin Asiya da Fasifik ba zai taba zama sansanin aiwatar da siyasar shiyya ba, ballantana ya shiga wani sabon yanayi na “Cacar baka”, ko zama fagen fito na fito. Ya zama wajibi mu rungumi yanayin bude kofa na yankin mu, kuma sannu a hankali mu wanzar da tsarin ingiza matakan kafa yankin ciniki maras shinge na Asiya da Fasifik, da hade sassan tattalin arzikin yankin, kana mu samar da budadden tsarin tattalin arziki na Asiya da Fasifik ta hanyar hadin gwiwar cimma moriya tare.
Xi ya jaddada cewa, tun farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar Sin na ci gaba da murmurewa, kuma ana kara samar da ci gaba mai inganci, al’amarin da ya sa har yanzu Sin ta zama kasa mafi girma ga ci gaban duk duniya. Ya ce, “Bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na dogon lokaci, bai sauya ba, kana ba zai sauya ba. Muna da yakini da kwarewa sosai wajen samar da ci gaba mai dorewa, kana kuma sabon ci gaban kasar Sin zai kara samar da sabon kuzari, da sabbin damammaki ga duk duniya. Kasar Sin na kokarin raya kanta, da fadada bude kofarta ga kasashen waje, da himmatuwa wajen kirkiro wani yanayin kasuwanci na bin doka da oda, wanda ya shafi kasa da kasa, al’amarin da ba zai sauya ba, kana kuma kasar ba za ta sauya manufarta ta samar da kyawawan hidimomi ga baki masu zuba jari ba. Babban makasudin zamanantar da kasar Sin bisa salon kanta shi ne, kara samar da jin dadi ga al’ummar kasar da yawansu ya zarce biliyan 1.4, wanda zai samar da babbar kasuwa, da zarafin hadin-gwiwa ga duk duniya, da sanya babban kuzari ga zamanantar da duniya baki daya”.
Xi ya kuma yi maraba da mutane daga bangarorin masana’antu da cinikayya na duk duniya, su shiga cikin kokarin zamanantar da kasar Sin, don more damammakin ci gaban kasar mai inganci.(Saminu Alhassan, Murtala Zhang)

 

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Liyafar Da Aka Shirya Masa A San Francisco

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.