• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

People walk past APEC Summit signage displayed at Moscone North on Monday, Nov. 13, 2023, in San Francisco. (Lea Suzuki/San Francisco Chronicle via AP)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da rubutaccen jawabi ga taron jagororin masana’antu da kasuwanci na kungiyar hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik ko APEC a takaice, a birnin San Francisco na kasar Amurka.

Shugaba Xi ya ce shekaru 30 da suka gabata, jagororin yankin Asiya da Fasifik, bisa burin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba, sun gudanar da kwarya-kwaryar taro na farko na shugabannin APEC, da nufin ingiza ci gaba, da hade sassan tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik da na sauran sassan duniya, ta yadda hakan ya dora yankin kan turba ta gaggauta samun ci gaba, tare da taimakawa yankin wajen zama cibiyar bunkasar tattalin arzikin duniya.

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa,duniya ta shiga wani sabon lokaci na tangal tangal da sauye sauye, kana ina za a dosa wajen aiwatar da hadin gwiwar yankin Asiya da Pasifik nan da shekaru 30 masu zuwa, ta zama sabon batu dake jan hankali a wannan lokacin da muke ciki. Dole ne mu mara baya ga ainihin burin hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik ko APEC, kana mu ingiza sabon kuzari ga hadin gwiwar kungiyar.

Ya kara da cewa, ya zama wajibi mu hada karfi da karfe wajen tabbatar da nasarar manufofi, da ka’idojin dake kunshe cikin tsarin dokokin MDD, mu nacewa turbar tattaunawa ba tare da fito na fito ba, mu wanzar da ci gaba da daidaito a yankin Asiya da Fasifik. Bai dace ba, kuma yankin Asiya da Fasifik ba zai taba zama sansanin aiwatar da siyasar shiyya ba, ballantana ya shiga wani sabon yanayi na “Cacar baka”, ko zama fagen fito na fito. Ya zama wajibi mu rungumi yanayin bude kofa na yankin mu, kuma sannu a hankali mu wanzar da tsarin ingiza matakan kafa yankin ciniki maras shinge na Asiya da Fasifik, da hade sassan tattalin arzikin yankin, kana mu samar da budadden tsarin tattalin arziki na Asiya da Fasifik ta hanyar hadin gwiwar cimma moriya tare.
Xi ya jaddada cewa, tun farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar Sin na ci gaba da murmurewa, kuma ana kara samar da ci gaba mai inganci, al’amarin da ya sa har yanzu Sin ta zama kasa mafi girma ga ci gaban duk duniya. Ya ce, “Bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na dogon lokaci, bai sauya ba, kana ba zai sauya ba. Muna da yakini da kwarewa sosai wajen samar da ci gaba mai dorewa, kana kuma sabon ci gaban kasar Sin zai kara samar da sabon kuzari, da sabbin damammaki ga duk duniya. Kasar Sin na kokarin raya kanta, da fadada bude kofarta ga kasashen waje, da himmatuwa wajen kirkiro wani yanayin kasuwanci na bin doka da oda, wanda ya shafi kasa da kasa, al’amarin da ba zai sauya ba, kana kuma kasar ba za ta sauya manufarta ta samar da kyawawan hidimomi ga baki masu zuba jari ba. Babban makasudin zamanantar da kasar Sin bisa salon kanta shi ne, kara samar da jin dadi ga al’ummar kasar da yawansu ya zarce biliyan 1.4, wanda zai samar da babbar kasuwa, da zarafin hadin-gwiwa ga duk duniya, da sanya babban kuzari ga zamanantar da duniya baki daya”.
Xi ya kuma yi maraba da mutane daga bangarorin masana’antu da cinikayya na duk duniya, su shiga cikin kokarin zamanantar da kasar Sin, don more damammakin ci gaban kasar mai inganci.(Saminu Alhassan, Murtala Zhang)

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSan FranciscoShugabashugaban kasar Sin Xi JinpingXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Kai Ziyara Saudiyya Da Guinea Bissau

Next Post

Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

5 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

6 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

13 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

13 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

16 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

17 hours ago
Next Post
Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.