• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

by Leadership Hausa
8 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Bala Mohammed, Gwamnan Jihar Bauchi, ya samu lambar yabo ta Leadership ta Gwamnan Shekara ta 2024.

Gwamna Bala ya samu wannan lambar yabo saboda irin sauye-sauyen da ya kawo a ɓangarori daban-daban, ciki har da ababen more rayuwa da ilimi da lafiya da kuma tsaro. Wannan shi ne karo na biyu da aka karrama shi da wannan lambar yabo saboda jagorancinsa mai cike da hangen nesa da sadaukar da kai wajen bunƙasa rayuwar jama’a.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Tarihi da Siyasa A Taƙaice

An haifi Bala Mohammed a Duguri, Alkaleri Jihar Bauchi, a ranar 5 ga Oktoba, 1958. Ya yi karatu a shashen harsuna na Jami’ar Maiduguri, sannan ya fara aikinsa a matsayin ɗan jarida, inda ya yi aiki a kamfanin dillancin labarai na ƙasa (News Agency of Nigeria), da wasu kafafen irinsu The Mirage da Democrat. A matsayinsa na ɗan jarida, ya gina fahimta sosai kan matsalolin da suka shafi jama’a, wanda ya ja hankalinsa zuwa shiga siyasa.

Bala, Ya fara siyasarsa a 2007, tsohon ɗan siyasa, ya zama Sanatan Bauchi ta Kudu, inda ya yi fice wajen gabatar da ƙudirori kan ayyukan gwamnati da yaƙi da cin hanci da rashawa. A 2010, ya zama Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kawo sauye-sauye a harkokin sufuri da gidaje da kula da muhalli. Daga cikin muhimman nasarorin da ya samu akwai ƙaddamar da hanyar sufurin jirgin ƙasa (Abuja Rail Mass Transit System), wanda ya rage cunkoso a birnin Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

A 2019, Bala Mohammed ya zama gwamnan Jihar Bauchi, inda ya mayar da hankali kan inganta rayuwar jama’a ta hanyar ayyukan ci gaba a fannonin ilimi da lafiya da noma da bunƙasa fannin tsaro.

Ilimi da Lafiya

Gwamnatin Kauran Bauchi ta gina tareq da gyara ajujuwa sama da 5,000, sannan ya rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta daga miliyan 1.2 zuwa 521,000. A ɓangaren lafiya kuwa ya gyara tare da gina sababbin asibitoci da cibiyoyin lafiya sama da 1,000, inda ya hakan samar da sauƙi ga al’ummar karkara wajen samun kulawa a fannin lafiya.

Ababen More Rayuwa da Noma

A ƙarƙashin mulkinsa, Ƙauran Bauchi ya gina sababbin hanyoyi da gadoji da hanyoyin karkara, ciki har da gadojin sama guda biyu a tsakiyar birnin jihar Bauchi, don rage cunkoson ababen hawa. Ya tallafa wa manoma ta hanyar rage farashin taki da kayan aikin gona da ba su horo kan fasahohin zamani, wanda hakan ya ƙara samar da yawan abinci da ayyukan yi a jihar.

Tallafi ga Mata da Matasa

A ƙarƙashin shirin Kaura Economic Empowerment Programme (KEEP), an samar da jari da bayar da horo ga matasa da mata don su kafa ƙananan sana’o’i. Kazalika, ya bayar da tallafin Keke NAPEP sama da 1,000 ga matasa ba tare da sanya ƙarin kuɗaɗe ba, don su samu damar dogaro da kansu.

Sanata Bala Mohammed, gwamna ne mai ƙwazo da himma wajen ziyartar wuraren aiki da sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a. Wannan salon jagoranci ya kawo amincewa daga jama’ar da ya ke mulka, inda suke ganinsa a matsayin jagora da ke kula da buƙatunsu.

A yau, Jihar Bauchi ta zama ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Nijeriya. Gwamna Bala Mohammed ya gina rayuwar jama’a ta hanyar bijiro da ayyukan ci gaba da kawo ci gaba mai ɗorewa, ya mayar da Jihar Bauchi jiha abar koyi a Arewacin Nijeriya. Wannan nasarar ta fito fili daga irin hangen nesansa na shugabanci, tare da aiki tuƙuru da bayar da kulawarsa ga buƙatun jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiBala Kauran BauchiBauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Next Post

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

3 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

9 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

11 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

11 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

14 hours ago
Next Post
Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.