ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

by Leadership Hausa
2 years ago
Bala Mohammed

Sanata Bala Mohammed, Gwamnan Jihar Bauchi, ya samu lambar yabo ta Leadership ta Gwamnan Shekara ta 2024.

Gwamna Bala ya samu wannan lambar yabo saboda irin sauye-sauyen da ya kawo a ɓangarori daban-daban, ciki har da ababen more rayuwa da ilimi da lafiya da kuma tsaro. Wannan shi ne karo na biyu da aka karrama shi da wannan lambar yabo saboda jagorancinsa mai cike da hangen nesa da sadaukar da kai wajen bunƙasa rayuwar jama’a.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Tarihi da Siyasa A Taƙaice

ADVERTISEMENT

An haifi Bala Mohammed a Duguri, Alkaleri Jihar Bauchi, a ranar 5 ga Oktoba, 1958. Ya yi karatu a shashen harsuna na Jami’ar Maiduguri, sannan ya fara aikinsa a matsayin ɗan jarida, inda ya yi aiki a kamfanin dillancin labarai na ƙasa (News Agency of Nigeria), da wasu kafafen irinsu The Mirage da Democrat. A matsayinsa na ɗan jarida, ya gina fahimta sosai kan matsalolin da suka shafi jama’a, wanda ya ja hankalinsa zuwa shiga siyasa.

Bala, Ya fara siyasarsa a 2007, tsohon ɗan siyasa, ya zama Sanatan Bauchi ta Kudu, inda ya yi fice wajen gabatar da ƙudirori kan ayyukan gwamnati da yaƙi da cin hanci da rashawa. A 2010, ya zama Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kawo sauye-sauye a harkokin sufuri da gidaje da kula da muhalli. Daga cikin muhimman nasarorin da ya samu akwai ƙaddamar da hanyar sufurin jirgin ƙasa (Abuja Rail Mass Transit System), wanda ya rage cunkoso a birnin Abuja.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

A 2019, Bala Mohammed ya zama gwamnan Jihar Bauchi, inda ya mayar da hankali kan inganta rayuwar jama’a ta hanyar ayyukan ci gaba a fannonin ilimi da lafiya da noma da bunƙasa fannin tsaro.

Ilimi da Lafiya

Gwamnatin Kauran Bauchi ta gina tareq da gyara ajujuwa sama da 5,000, sannan ya rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta daga miliyan 1.2 zuwa 521,000. A ɓangaren lafiya kuwa ya gyara tare da gina sababbin asibitoci da cibiyoyin lafiya sama da 1,000, inda ya hakan samar da sauƙi ga al’ummar karkara wajen samun kulawa a fannin lafiya.

Ababen More Rayuwa da Noma

A ƙarƙashin mulkinsa, Ƙauran Bauchi ya gina sababbin hanyoyi da gadoji da hanyoyin karkara, ciki har da gadojin sama guda biyu a tsakiyar birnin jihar Bauchi, don rage cunkoson ababen hawa. Ya tallafa wa manoma ta hanyar rage farashin taki da kayan aikin gona da ba su horo kan fasahohin zamani, wanda hakan ya ƙara samar da yawan abinci da ayyukan yi a jihar.

Tallafi ga Mata da Matasa

A ƙarƙashin shirin Kaura Economic Empowerment Programme (KEEP), an samar da jari da bayar da horo ga matasa da mata don su kafa ƙananan sana’o’i. Kazalika, ya bayar da tallafin Keke NAPEP sama da 1,000 ga matasa ba tare da sanya ƙarin kuɗaɗe ba, don su samu damar dogaro da kansu.

Sanata Bala Mohammed, gwamna ne mai ƙwazo da himma wajen ziyartar wuraren aiki da sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a. Wannan salon jagoranci ya kawo amincewa daga jama’ar da ya ke mulka, inda suke ganinsa a matsayin jagora da ke kula da buƙatunsu.

A yau, Jihar Bauchi ta zama ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Nijeriya. Gwamna Bala Mohammed ya gina rayuwar jama’a ta hanyar bijiro da ayyukan ci gaba da kawo ci gaba mai ɗorewa, ya mayar da Jihar Bauchi jiha abar koyi a Arewacin Nijeriya. Wannan nasarar ta fito fili daga irin hangen nesansa na shugabanci, tare da aiki tuƙuru da bayar da kulawarsa ga buƙatun jama’a.

Bala Mohammed
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.