• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

by Muhammad and Leadership Hausa
7 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fasto Umo Bassey Eno ya samu lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekara ta 2024 ta Jaridar Leadership, saboda jagorancinsa na hangen nesa da kuma saurin aiwatar da tsare-tsaren Noma da Ci gaban Karkara da samar da Ababen More Rayuwa, Tsaro da Ƙarfafa Wa Jama’ar jiharsa (ARISE Agenda).

Wannan Shiri (ARISE Agenda) ya shafi ɓangarori masu muhimmanci kamar lafiya da ilimiilimi da tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi da sauransu, wanda ya hakan ya yi tasiri a Jihar Akwa Ibom cikin watanni 15 kacal na mulkinsa. Ta hanyar ayyana muradunsa a fili da cimma nasarori masu gamsarwa, Fasto Eno, ya tabbatar da cancantarsa na samu wannan babbar lambar yabo.

  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Umo Eno shi ne gwamnan farar hula na huɗu a tarihin Jihar Akwa Ibom mai shekaru 37 tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a shekarar 1999. Fasto ne a Cocin All Nations Ministry International Church, bayyanarsa a matsayin gwamna abin mamaki ne, wanda ya sa ake masa laƙani da “Golden Boy” saboda kyawun fuskarsa da kuma tafiyar siyasarsa mai cike da al’ajabi. An gano bajintarsa a siyasance ta hannun, tsohon Gwamna Udom Emmanuel, wanda Eno ya fara siyasarsa ta hanyar zama Kwamishinan filaye a jihar.

A lokacin da tsohon Gwamna Udom Emmanuel ya kusa barin mulki, ba tare da ɓata lokaci ba ya zaɓi Eno a matsayin wanda zai gaje shi duk da yawan masu neman wannan matsayi. Wannan sanarwa ta girgiza mutane da dama da suke tsammanin zaɓar wanda ya yi fice a siyasar jihar. Duk da haka, Eno ya samu karɓuwa sosai, ba kawai daga Kiristoci da abokan tsohon gwamnan ba, har ma daga jama’ar Akwa Ibom da yawansu ya kai miliyan 7.2. Duk da cewa akwai shakku a zukatan wasu saboda rashin daɗewarsa a harkar siyasa, amma ya kawar da wannan shakkun ta hanyar juriya da jagorancinsa.

Ko da yake ya fuskanci zarge-zarge a siyasa, ciki har da kiransa da “wanda bai da ilimi,” Eno ya fuskanci kalubalen, ta hanyar jajircewa da ƙwarewa a matsayinsa na shugaba. Tafiyarsa a harkar siyasa, wanda ba kasafai aka san shi da ita ba, ta zama misalin yadda mutum zai iya nasara duk da ƙalubalen da zai fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

A ranar 29 ga watan Mayu, 2023, lokacin rantsar da shi, Eno ya bayar da labarin rayuwarsa mai ban sha’awa, inda ya ruwaito yadda ya tashi cikin ƙunci a matsayin ɗan wani ɗan sanda da kuma mahaifiya mai ƙoƙarin kula da iyalanta bayan mutuwar mahaifinsa. Ya tashi a barikin ‘yansanda, ya yi karatu da sayar da lemo a Filin Jirgin Sama na Legas domin tallafa wa mahaifiyarsa da ‘yan uwansa. Ya ruwaito cewar, “Da wani ya faɗa min zan zama gwamna, da na ce masa ya je asibiti domin tabbas yana fama da ciwon maleriya mai tsanani ko kuma ya ruɗe.” Yau, mutumin da ya tashi a wannan yanayi ya zama gwamnan Jihar Akwa Ibom a zahiri.”

Mulkin Eno ya tabbatar da alƙawarin jagoransa, Udom Emmanuel, wanda ya ce, “Mutumin da zai zo bayana zai yi abubuwa masu tasiri sama da waɗanda na yi.” Ta hanyar tsarin ARISE Agenda, Gwamna Eno ya mayar da hankali kan samar da abinci da samar da ayyukan yi da kuma samar da tsaro mai inganci, wanda ya mayar da Akwa Ibom wata mafaka ga masu yawon buɗe ido da masu zuba jari da kuma baƙi.

Wannan ci gaba ya bunƙasa samun kuɗaɗen shiga na jihar, wanda ya ƙara mata matsayi a matsayin babbar jiha mai arziƙi a yankin Neja Delta.

Nasarar da Gwamna Eno ya samu ta ja hankalin mutane da dama, har ma a matakin ƙasa. Duk da cewa Akwa Ibom tana ƙarƙashin mulkin jam’iyyar adawa, ya samu haɗin kai daga manyan mutane irin su Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio. Jagorancinsa ya kawo ƙarshen rigingimun siyasa da suka daɗe suna hana Jihar Akwa Ibom samun ayyukan gwamnatin tarayya da wasu tallafi, inda ya kawo wani sabon salo na haɗin kai da ci gaba a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiUmo Bassey Eno
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Next Post

Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu’amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

14 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

17 hours ago
Next Post
Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu’amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu'amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.