ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

by Muhammad and Leadership Hausa
2 years ago
Umo Bassey Eno

Fasto Umo Bassey Eno ya samu lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekara ta 2024 ta Jaridar Leadership, saboda jagorancinsa na hangen nesa da kuma saurin aiwatar da tsare-tsaren Noma da Ci gaban Karkara da samar da Ababen More Rayuwa, Tsaro da Ƙarfafa Wa Jama’ar jiharsa (ARISE Agenda).

Wannan Shiri (ARISE Agenda) ya shafi ɓangarori masu muhimmanci kamar lafiya da ilimiilimi da tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi da sauransu, wanda ya hakan ya yi tasiri a Jihar Akwa Ibom cikin watanni 15 kacal na mulkinsa. Ta hanyar ayyana muradunsa a fili da cimma nasarori masu gamsarwa, Fasto Eno, ya tabbatar da cancantarsa na samu wannan babbar lambar yabo.

  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Umo Eno shi ne gwamnan farar hula na huɗu a tarihin Jihar Akwa Ibom mai shekaru 37 tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a shekarar 1999. Fasto ne a Cocin All Nations Ministry International Church, bayyanarsa a matsayin gwamna abin mamaki ne, wanda ya sa ake masa laƙani da “Golden Boy” saboda kyawun fuskarsa da kuma tafiyar siyasarsa mai cike da al’ajabi. An gano bajintarsa a siyasance ta hannun, tsohon Gwamna Udom Emmanuel, wanda Eno ya fara siyasarsa ta hanyar zama Kwamishinan filaye a jihar.

ADVERTISEMENT

A lokacin da tsohon Gwamna Udom Emmanuel ya kusa barin mulki, ba tare da ɓata lokaci ba ya zaɓi Eno a matsayin wanda zai gaje shi duk da yawan masu neman wannan matsayi. Wannan sanarwa ta girgiza mutane da dama da suke tsammanin zaɓar wanda ya yi fice a siyasar jihar. Duk da haka, Eno ya samu karɓuwa sosai, ba kawai daga Kiristoci da abokan tsohon gwamnan ba, har ma daga jama’ar Akwa Ibom da yawansu ya kai miliyan 7.2. Duk da cewa akwai shakku a zukatan wasu saboda rashin daɗewarsa a harkar siyasa, amma ya kawar da wannan shakkun ta hanyar juriya da jagorancinsa.

Ko da yake ya fuskanci zarge-zarge a siyasa, ciki har da kiransa da “wanda bai da ilimi,” Eno ya fuskanci kalubalen, ta hanyar jajircewa da ƙwarewa a matsayinsa na shugaba. Tafiyarsa a harkar siyasa, wanda ba kasafai aka san shi da ita ba, ta zama misalin yadda mutum zai iya nasara duk da ƙalubalen da zai fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A ranar 29 ga watan Mayu, 2023, lokacin rantsar da shi, Eno ya bayar da labarin rayuwarsa mai ban sha’awa, inda ya ruwaito yadda ya tashi cikin ƙunci a matsayin ɗan wani ɗan sanda da kuma mahaifiya mai ƙoƙarin kula da iyalanta bayan mutuwar mahaifinsa. Ya tashi a barikin ‘yansanda, ya yi karatu da sayar da lemo a Filin Jirgin Sama na Legas domin tallafa wa mahaifiyarsa da ‘yan uwansa. Ya ruwaito cewar, “Da wani ya faɗa min zan zama gwamna, da na ce masa ya je asibiti domin tabbas yana fama da ciwon maleriya mai tsanani ko kuma ya ruɗe.” Yau, mutumin da ya tashi a wannan yanayi ya zama gwamnan Jihar Akwa Ibom a zahiri.”

Mulkin Eno ya tabbatar da alƙawarin jagoransa, Udom Emmanuel, wanda ya ce, “Mutumin da zai zo bayana zai yi abubuwa masu tasiri sama da waɗanda na yi.” Ta hanyar tsarin ARISE Agenda, Gwamna Eno ya mayar da hankali kan samar da abinci da samar da ayyukan yi da kuma samar da tsaro mai inganci, wanda ya mayar da Akwa Ibom wata mafaka ga masu yawon buɗe ido da masu zuba jari da kuma baƙi.

Wannan ci gaba ya bunƙasa samun kuɗaɗen shiga na jihar, wanda ya ƙara mata matsayi a matsayin babbar jiha mai arziƙi a yankin Neja Delta.

Nasarar da Gwamna Eno ya samu ta ja hankalin mutane da dama, har ma a matakin ƙasa. Duk da cewa Akwa Ibom tana ƙarƙashin mulkin jam’iyyar adawa, ya samu haɗin kai daga manyan mutane irin su Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio. Jagorancinsa ya kawo ƙarshen rigingimun siyasa da suka daɗe suna hana Jihar Akwa Ibom samun ayyukan gwamnatin tarayya da wasu tallafi, inda ya kawo wani sabon salo na haɗin kai da ci gaba a jihar.

Umo Bassey Eno
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Umo Bassey Eno
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu’amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu'amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.