ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

by Muhammad and Leadership Hausa
2 years ago
Bashir Adewale Adeniyi

Jagorancin Alhaji Bashir Adewale Adeniyi a matsayin Shugaban Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), ya kawo sauye-sauye masu matuƙar tasiri, inda ya samar da zaman lafiya da inganta aiki da ƙaruwar kuɗaɗen shiga. Wannan nasara ta taimaka matuƙa wajen bunƙasar tattalin arziƙin Nijeriya, wanda ya sa aka zaɓe shi a matsayin Gwarzon Ma’aikaci Na Shekarar 2024.

Tun bayan naɗa shi muƙamin a watan Yunin 2023, Adeniyi ya fuskanci manyan matsaloli a hukumar, wanda suka haɗa da rashin ƙwarewar aiki da cin hanci da rashawa, da tsofaffin hanyoyin aiki. Ta hanyar amfani da hangen nesa da ƙwazo, ya bijiro da sababbin tsare-tsare a hukumar, wanda ya nuna yadda za a iya kawo gyare-gyare masu kyau a ɓangaren ayyukan gwamnati a Nijeriya.

  • Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Dabarun Adeniyi sun fi mayar da hankali kan sauƙaƙa ayyukan Kwastam da kuma inganta kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyensa shi ne rage yawan tawagar da hukumar ke da su, inda ya haɗe rundunar Strike Force Teams da Federal Operations Unit (FOU). Wannan ya rage yawan shingen bincike daga biyar zuwa biyu a kowace hanya, wanda ya sauƙaƙa harkokin kasuwanci kuma ya rage cin hanci a kan iyaka. Wannan gyara ya ƙara wanzar da gaskiya a aikin hukumar tare da tallafa wa kasuwanci, inda ya kafa sabon mizanin inganta aiki.

A ƙarƙashin shugabancinsa, hukumar NCS ta ƙarfafa haɗin guiwar ƙasa da ƙasa, musamman da Ƙungiyar Kwastam ta Duniya (WCO), don tabbatar da amfani da kyawawan ƙa’idojin aiki na ƙasa da ƙasa. Adeniyi ya kuma mayar da hankali kan tsaro a iyakokin ƙasa ta hanyar samar da sabbin dabaru, kamar sayen jirgin sama ƙirar Cessna Grand Caravan EX-208B domin bincike ta sama. Wannan jirgin ya inganta aikin sintiri a wuraren da ke da wahalar zuwa, wanda ya bunƙasa yaƙi da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Sabunta fasaha shi ma wani ginshiƙi ne a jagorancin Adeniyi. Ya jagoranci shirye-shirye irin su Authorized Economic Operators (AEO), wanda ya sauƙaƙa aikin Kwastam ga ‘yan kasuwa masu bin doka tare da ƙara musu damar yin gogayya a kasuwannin duniya.

Ƙaddamar da Time Release Study (TRS) da amfani da fasahar geospatial ya ƙara tabbatar da jajircewarsa wajen amfani da fasaha domin inganta aiki da samun sahihanci.

Waɗannan sauye-sauye sun haifar da sakamako mai tasirin gaske a fannin tattalin arziƙi. Kuɗaɗen shiga na wata-wata sun ƙaru da kashi 70.13, daga Naira biliyan 202 zuwa sama da Naira biliyan 343.

A shekarar 2023, duk da ragi da aka samu a harkokin kasuwanci, hukumar ta samu jimillar kuɗin shiga har Naira tiriliyan 3.2, wanda hakan ya ƙaru da kashi 21.4 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, wannan ya nuna cewa Adeniyi ya inganta kuɗaɗen gwamnati ta hanyar samar da tsari mai inganci.

Bugu da ƙari, Adeniyi ya ƙara ƙarfi a ɓangaren aiwatar da dokoki. A shekarar 2023 kaɗai, hukumar ta kama kayayyaki 1,763 da darajar kuɗinsu ta kai Naira biliyan 11.9 a matsayin kuɗin haraji, tare da gurfanar da mutane 52. Wannan tsauraran matakai sun ƙara tabbatar da sadaukarwarsa wajen kare tattalin arziƙin Nijeriya daga illolin safarar kayan haram.

Duk da waɗannan nasarori, Adeniyi ya ci gaba da duba yadda zai ƙara inganta harkokin kasuwanci. Burinsa na gaba ya haɗa da samar da sabbin dabarun aiki a iyakoki, gyara tsarin TRS da shirye-shiryen AEO, tare da rage jinkiri a harkokin gwamnati.

Haka kuma yana ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan illolin da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba ke yi wa tattalin arziƙi, tare da tabbatar da Nijeriya ta samu matsayi mai kyau a kasuwannin duniya.

Jagorancin Adeniyi ya zama misali a tsakanin shugabannin ma’aikatun gwamnati, wanda hakan ya sa ya cancanci wannan lambar yabo daga Jaridar Leadership

Bashir Adewale Adeniyi
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Bashir Adewale Adeniyi
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.