ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

by Muhammad and Leadership Hausa
2 years ago
Bashir Adewale Adeniyi

Jagorancin Alhaji Bashir Adewale Adeniyi a matsayin Shugaban Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), ya kawo sauye-sauye masu matuƙar tasiri, inda ya samar da zaman lafiya da inganta aiki da ƙaruwar kuɗaɗen shiga. Wannan nasara ta taimaka matuƙa wajen bunƙasar tattalin arziƙin Nijeriya, wanda ya sa aka zaɓe shi a matsayin Gwarzon Ma’aikaci Na Shekarar 2024.

Tun bayan naɗa shi muƙamin a watan Yunin 2023, Adeniyi ya fuskanci manyan matsaloli a hukumar, wanda suka haɗa da rashin ƙwarewar aiki da cin hanci da rashawa, da tsofaffin hanyoyin aiki. Ta hanyar amfani da hangen nesa da ƙwazo, ya bijiro da sababbin tsare-tsare a hukumar, wanda ya nuna yadda za a iya kawo gyare-gyare masu kyau a ɓangaren ayyukan gwamnati a Nijeriya.

  • Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Dabarun Adeniyi sun fi mayar da hankali kan sauƙaƙa ayyukan Kwastam da kuma inganta kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyensa shi ne rage yawan tawagar da hukumar ke da su, inda ya haɗe rundunar Strike Force Teams da Federal Operations Unit (FOU). Wannan ya rage yawan shingen bincike daga biyar zuwa biyu a kowace hanya, wanda ya sauƙaƙa harkokin kasuwanci kuma ya rage cin hanci a kan iyaka. Wannan gyara ya ƙara wanzar da gaskiya a aikin hukumar tare da tallafa wa kasuwanci, inda ya kafa sabon mizanin inganta aiki.

A ƙarƙashin shugabancinsa, hukumar NCS ta ƙarfafa haɗin guiwar ƙasa da ƙasa, musamman da Ƙungiyar Kwastam ta Duniya (WCO), don tabbatar da amfani da kyawawan ƙa’idojin aiki na ƙasa da ƙasa. Adeniyi ya kuma mayar da hankali kan tsaro a iyakokin ƙasa ta hanyar samar da sabbin dabaru, kamar sayen jirgin sama ƙirar Cessna Grand Caravan EX-208B domin bincike ta sama. Wannan jirgin ya inganta aikin sintiri a wuraren da ke da wahalar zuwa, wanda ya bunƙasa yaƙi da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Sabunta fasaha shi ma wani ginshiƙi ne a jagorancin Adeniyi. Ya jagoranci shirye-shirye irin su Authorized Economic Operators (AEO), wanda ya sauƙaƙa aikin Kwastam ga ‘yan kasuwa masu bin doka tare da ƙara musu damar yin gogayya a kasuwannin duniya.

Ƙaddamar da Time Release Study (TRS) da amfani da fasahar geospatial ya ƙara tabbatar da jajircewarsa wajen amfani da fasaha domin inganta aiki da samun sahihanci.

Waɗannan sauye-sauye sun haifar da sakamako mai tasirin gaske a fannin tattalin arziƙi. Kuɗaɗen shiga na wata-wata sun ƙaru da kashi 70.13, daga Naira biliyan 202 zuwa sama da Naira biliyan 343.

A shekarar 2023, duk da ragi da aka samu a harkokin kasuwanci, hukumar ta samu jimillar kuɗin shiga har Naira tiriliyan 3.2, wanda hakan ya ƙaru da kashi 21.4 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, wannan ya nuna cewa Adeniyi ya inganta kuɗaɗen gwamnati ta hanyar samar da tsari mai inganci.

Bugu da ƙari, Adeniyi ya ƙara ƙarfi a ɓangaren aiwatar da dokoki. A shekarar 2023 kaɗai, hukumar ta kama kayayyaki 1,763 da darajar kuɗinsu ta kai Naira biliyan 11.9 a matsayin kuɗin haraji, tare da gurfanar da mutane 52. Wannan tsauraran matakai sun ƙara tabbatar da sadaukarwarsa wajen kare tattalin arziƙin Nijeriya daga illolin safarar kayan haram.

Duk da waɗannan nasarori, Adeniyi ya ci gaba da duba yadda zai ƙara inganta harkokin kasuwanci. Burinsa na gaba ya haɗa da samar da sabbin dabarun aiki a iyakoki, gyara tsarin TRS da shirye-shiryen AEO, tare da rage jinkiri a harkokin gwamnati.

Haka kuma yana ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan illolin da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba ke yi wa tattalin arziƙi, tare da tabbatar da Nijeriya ta samu matsayi mai kyau a kasuwannin duniya.

Jagorancin Adeniyi ya zama misali a tsakanin shugabannin ma’aikatun gwamnati, wanda hakan ya sa ya cancanci wannan lambar yabo daga Jaridar Leadership

Bashir Adewale Adeniyi
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Bashir Adewale Adeniyi
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.