• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

by Leadership Hausa
10 months ago
in Labarai
0
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dame (Dr.) Adaora Umeoji, ita ce manajan darakta kuma shugabar Bankin Zenith Plc, tun daga watan Yunin 2024 har zuwa yanzu, ta samu wannan lambar yabon ta Leadership saboda kyakkyawan jagoranci da ƙwarewa da kuma sadaukarwarta wajen tabbatar ingantaccen tsarin tafiyar da harkokin banki.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi gagarumar nasara a kai, sun haɗa da kafa tarihin samar da riba a ƙarƙashin jagorancinta, inda Bankin Zenith, ya samu naira tiriliyan ɗaya cikin watanni tara na farkon shekarar 2024, samun ƙaruwar kashi 98.57% hakan ke nuna samun ƙarin riba kan yadda aka saba samu a duk shekara, a ɗayan bangaren kuma babbar ribar bankin ta kai Naira tiriliyan 2.8, yadda hakan ke nuna samun ƙaruwar kashi 118.16%.

  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya
  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar

Umeoji, ta yi nasarar zamanantar da tsarin harkokin bankin tare da faɗaɗa damar hada-hadar kuɗaɗe ta fuskar amfani da kididdigar jama’a don fahimtar abin da kowanne rukuni na jama’a ke buƙata, wannan mataki ya ƙara wa Bankin Zenith karɓuwa a matsayin jagora kuma abin amincewa ga masana’antu a harkokinsu.

Ta yi amfani da ƙwarewa a jagoranci da hangen nesa ta hanyar amfani da gogewar da take da ita na sama da shekaru 30 a aikin banki, ciki har da shafe shekaru 26 da ta yi a Bankin Zenith, inda ta samar da ci gaba wajen kyautata tsarin aiki da kawo sababbin dabaru don inganta hulɗa da abokon kasuwanci da janyo hankalin sauran jama’a ga bankin.

Tarin Ilimi da ficen da shugabar ta yi a ɓangarori daban-daban wajen samun shaidun karatu da dama da suka haɗa da digirin digirgir kan gudanar da kasuwanci daga Jami’ar Harvard na Columbia da makarantar MIT, ta kuma kasance ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar ƙwararrun ma’aikatan bankuna na Ingila, sai kuma manyan shaidun karramawa da ta samu a Nijeriya, da kuma ta babbar hadima a majami’ar St. Sylvester.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Umeoji, ta kasance mace mai ɗa’a da martaba ɗabi’un aikin banki musamman a matsayinta na wadda ta kafa ƙungiyar mabiya Katolika na Ma’aikatan Banki ta Nijeriya (CBAN), inda take bayar da shawarwari kan harkokin banki da cinikayya ta yadda al’umma za su amfana daga tarin iliminta da ƙwarewarta.

A.taƙaice dai, ko shakka babu jagorancin Umeoji, yana nuni da irin tsayuwar dakar da take wajen ƙirƙire-ƙirƙire da fito da sababbin dabaru da kuma mayar da hankali wajen sanya harkar banki ta kasance mai tasiri, musamman a bangaren hada-hadar kuɗi na ƙasarnan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiDame (Dr.) Adaora Umeoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Ci Gaba Da Karfafa Horar Da Sojoji Don Dakile Yunkurin Neman “’Yancin Kan Taiwan”

Next Post

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

Related

Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

27 minutes ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

1 hour ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

2 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

3 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

4 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

6 hours ago
Next Post
Olori Atuwatse III

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al'umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.