• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

by Leadership Hausa
8 months ago
in Labarai
0
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dame (Dr.) Adaora Umeoji, ita ce manajan darakta kuma shugabar Bankin Zenith Plc, tun daga watan Yunin 2024 har zuwa yanzu, ta samu wannan lambar yabon ta Leadership saboda kyakkyawan jagoranci da ƙwarewa da kuma sadaukarwarta wajen tabbatar ingantaccen tsarin tafiyar da harkokin banki.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi gagarumar nasara a kai, sun haɗa da kafa tarihin samar da riba a ƙarƙashin jagorancinta, inda Bankin Zenith, ya samu naira tiriliyan ɗaya cikin watanni tara na farkon shekarar 2024, samun ƙaruwar kashi 98.57% hakan ke nuna samun ƙarin riba kan yadda aka saba samu a duk shekara, a ɗayan bangaren kuma babbar ribar bankin ta kai Naira tiriliyan 2.8, yadda hakan ke nuna samun ƙaruwar kashi 118.16%.

  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya
  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar

Umeoji, ta yi nasarar zamanantar da tsarin harkokin bankin tare da faɗaɗa damar hada-hadar kuɗaɗe ta fuskar amfani da kididdigar jama’a don fahimtar abin da kowanne rukuni na jama’a ke buƙata, wannan mataki ya ƙara wa Bankin Zenith karɓuwa a matsayin jagora kuma abin amincewa ga masana’antu a harkokinsu.

Ta yi amfani da ƙwarewa a jagoranci da hangen nesa ta hanyar amfani da gogewar da take da ita na sama da shekaru 30 a aikin banki, ciki har da shafe shekaru 26 da ta yi a Bankin Zenith, inda ta samar da ci gaba wajen kyautata tsarin aiki da kawo sababbin dabaru don inganta hulɗa da abokon kasuwanci da janyo hankalin sauran jama’a ga bankin.

Tarin Ilimi da ficen da shugabar ta yi a ɓangarori daban-daban wajen samun shaidun karatu da dama da suka haɗa da digirin digirgir kan gudanar da kasuwanci daga Jami’ar Harvard na Columbia da makarantar MIT, ta kuma kasance ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar ƙwararrun ma’aikatan bankuna na Ingila, sai kuma manyan shaidun karramawa da ta samu a Nijeriya, da kuma ta babbar hadima a majami’ar St. Sylvester.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Umeoji, ta kasance mace mai ɗa’a da martaba ɗabi’un aikin banki musamman a matsayinta na wadda ta kafa ƙungiyar mabiya Katolika na Ma’aikatan Banki ta Nijeriya (CBAN), inda take bayar da shawarwari kan harkokin banki da cinikayya ta yadda al’umma za su amfana daga tarin iliminta da ƙwarewarta.

A.taƙaice dai, ko shakka babu jagorancin Umeoji, yana nuni da irin tsayuwar dakar da take wajen ƙirƙire-ƙirƙire da fito da sababbin dabaru da kuma mayar da hankali wajen sanya harkar banki ta kasance mai tasiri, musamman a bangaren hada-hadar kuɗi na ƙasarnan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiDame (Dr.) Adaora Umeoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Ci Gaba Da Karfafa Horar Da Sojoji Don Dakile Yunkurin Neman “’Yancin Kan Taiwan”

Next Post

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Olori Atuwatse III

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al'umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.