• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

by Leadership Hausa
7 months ago
in Labarai
0
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dame (Dr.) Adaora Umeoji, ita ce manajan darakta kuma shugabar Bankin Zenith Plc, tun daga watan Yunin 2024 har zuwa yanzu, ta samu wannan lambar yabon ta Leadership saboda kyakkyawan jagoranci da ƙwarewa da kuma sadaukarwarta wajen tabbatar ingantaccen tsarin tafiyar da harkokin banki.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi gagarumar nasara a kai, sun haɗa da kafa tarihin samar da riba a ƙarƙashin jagorancinta, inda Bankin Zenith, ya samu naira tiriliyan ɗaya cikin watanni tara na farkon shekarar 2024, samun ƙaruwar kashi 98.57% hakan ke nuna samun ƙarin riba kan yadda aka saba samu a duk shekara, a ɗayan bangaren kuma babbar ribar bankin ta kai Naira tiriliyan 2.8, yadda hakan ke nuna samun ƙaruwar kashi 118.16%.

  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya
  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar

Umeoji, ta yi nasarar zamanantar da tsarin harkokin bankin tare da faɗaɗa damar hada-hadar kuɗaɗe ta fuskar amfani da kididdigar jama’a don fahimtar abin da kowanne rukuni na jama’a ke buƙata, wannan mataki ya ƙara wa Bankin Zenith karɓuwa a matsayin jagora kuma abin amincewa ga masana’antu a harkokinsu.

Ta yi amfani da ƙwarewa a jagoranci da hangen nesa ta hanyar amfani da gogewar da take da ita na sama da shekaru 30 a aikin banki, ciki har da shafe shekaru 26 da ta yi a Bankin Zenith, inda ta samar da ci gaba wajen kyautata tsarin aiki da kawo sababbin dabaru don inganta hulɗa da abokon kasuwanci da janyo hankalin sauran jama’a ga bankin.

Tarin Ilimi da ficen da shugabar ta yi a ɓangarori daban-daban wajen samun shaidun karatu da dama da suka haɗa da digirin digirgir kan gudanar da kasuwanci daga Jami’ar Harvard na Columbia da makarantar MIT, ta kuma kasance ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar ƙwararrun ma’aikatan bankuna na Ingila, sai kuma manyan shaidun karramawa da ta samu a Nijeriya, da kuma ta babbar hadima a majami’ar St. Sylvester.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Umeoji, ta kasance mace mai ɗa’a da martaba ɗabi’un aikin banki musamman a matsayinta na wadda ta kafa ƙungiyar mabiya Katolika na Ma’aikatan Banki ta Nijeriya (CBAN), inda take bayar da shawarwari kan harkokin banki da cinikayya ta yadda al’umma za su amfana daga tarin iliminta da ƙwarewarta.

A.taƙaice dai, ko shakka babu jagorancin Umeoji, yana nuni da irin tsayuwar dakar da take wajen ƙirƙire-ƙirƙire da fito da sababbin dabaru da kuma mayar da hankali wajen sanya harkar banki ta kasance mai tasiri, musamman a bangaren hada-hadar kuɗi na ƙasarnan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiDame (Dr.) Adaora Umeoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Ci Gaba Da Karfafa Horar Da Sojoji Don Dakile Yunkurin Neman “’Yancin Kan Taiwan”

Next Post

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

8 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

10 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

11 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

13 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

13 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

16 hours ago
Next Post
Olori Atuwatse III

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al'umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.