ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

by Leadership Hausa
2 years ago
Adaora Umeoji

Dame (Dr.) Adaora Umeoji, ita ce manajan darakta kuma shugabar Bankin Zenith Plc, tun daga watan Yunin 2024 har zuwa yanzu, ta samu wannan lambar yabon ta Leadership saboda kyakkyawan jagoranci da ƙwarewa da kuma sadaukarwarta wajen tabbatar ingantaccen tsarin tafiyar da harkokin banki.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi gagarumar nasara a kai, sun haɗa da kafa tarihin samar da riba a ƙarƙashin jagorancinta, inda Bankin Zenith, ya samu naira tiriliyan ɗaya cikin watanni tara na farkon shekarar 2024, samun ƙaruwar kashi 98.57% hakan ke nuna samun ƙarin riba kan yadda aka saba samu a duk shekara, a ɗayan bangaren kuma babbar ribar bankin ta kai Naira tiriliyan 2.8, yadda hakan ke nuna samun ƙaruwar kashi 118.16%.

  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya
  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar

Umeoji, ta yi nasarar zamanantar da tsarin harkokin bankin tare da faɗaɗa damar hada-hadar kuɗaɗe ta fuskar amfani da kididdigar jama’a don fahimtar abin da kowanne rukuni na jama’a ke buƙata, wannan mataki ya ƙara wa Bankin Zenith karɓuwa a matsayin jagora kuma abin amincewa ga masana’antu a harkokinsu.

ADVERTISEMENT

Ta yi amfani da ƙwarewa a jagoranci da hangen nesa ta hanyar amfani da gogewar da take da ita na sama da shekaru 30 a aikin banki, ciki har da shafe shekaru 26 da ta yi a Bankin Zenith, inda ta samar da ci gaba wajen kyautata tsarin aiki da kawo sababbin dabaru don inganta hulɗa da abokon kasuwanci da janyo hankalin sauran jama’a ga bankin.

Tarin Ilimi da ficen da shugabar ta yi a ɓangarori daban-daban wajen samun shaidun karatu da dama da suka haɗa da digirin digirgir kan gudanar da kasuwanci daga Jami’ar Harvard na Columbia da makarantar MIT, ta kuma kasance ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar ƙwararrun ma’aikatan bankuna na Ingila, sai kuma manyan shaidun karramawa da ta samu a Nijeriya, da kuma ta babbar hadima a majami’ar St. Sylvester.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Umeoji, ta kasance mace mai ɗa’a da martaba ɗabi’un aikin banki musamman a matsayinta na wadda ta kafa ƙungiyar mabiya Katolika na Ma’aikatan Banki ta Nijeriya (CBAN), inda take bayar da shawarwari kan harkokin banki da cinikayya ta yadda al’umma za su amfana daga tarin iliminta da ƙwarewarta.

A.taƙaice dai, ko shakka babu jagorancin Umeoji, yana nuni da irin tsayuwar dakar da take wajen ƙirƙire-ƙirƙire da fito da sababbin dabaru da kuma mayar da hankali wajen sanya harkar banki ta kasance mai tasiri, musamman a bangaren hada-hadar kuɗi na ƙasarnan.

Adaora Umeoji
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Olori Atuwatse III

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al'umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.