• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin majalisar wakilai kan albartun kasa, ya ce Nijeriya tana tafka asarar naira biliyan 9 a kowace shekara sakamakon aikace-aikacen masu hakar ma’adinai ta haramtattun hanyoyi a Nijeriya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rundunar sojin Nijeriya ta ce, ta cafke wadanda take zargi da hannu a hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba su 387 a cikin watanni bakwai da suka gabata.

  • Ramin Haƙar Ma’adanai Ya Rufta Da Mutum 3 A Jihar Neja
  • Miyar Agushi Mai Dadi Irin Ta Yammacin Nijeriya

Shugaban kwamitin majalisar, Jonathan Gaza Gbefwi, shi ne ya shaida hakan a yayin taron jin bahasin jama’a da kwamitin ya shirya kan binciken lamuran da suka shafi hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da na albartun kasa. Ya ce, wannan mummunar ayyukan satar ma’adinai ya janyo takaituwar jin gajiyar albartun da jama’an kasa ba su yi yadda ya dace.

Ya koka kan cewa zallar kaso uku kawai cikin kamfanonin da ke hakar ma’adinai ne suka biya na kudin lasisi hakar ma’adinai a kasar nan.

A cewarsa, daga cikin illar da hako ma’adinai ta barauniyar hanya ke janyowa har da janyo matsalolin tsaro da kuma arangama kan wake ko su waye masu ikon jan ragamar wuraren hako ma’adinai da albartun da ke ciki.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Ya ce, irin wannan rigimar na fantsama har ya shafi siyasa da zamantakewar jama’an da ke yankunan da abun ya shafa, wanda hakan ba daidai ba ne sam.

Sannan ya kara da cewa taron jin bahasin an shirya ne da zimmar shawo kan matsalolin da suke tattare da aikace-aikacen hako ma’adinai da kuma inganta hanyoyin samar da lasisi domin kyautata samar wa kasar nan da kudaden shiga da kuma cin gajiyar ma’adinan da suke jibge a kasar ba tare da wasu matsaloli ba.

“Nijeriya tana rasa naira biliyan 9 a kowace shekara kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba. Don haka, jagorancin majalisar wakilai ta 10 ya ga dacewar ya ji bahasin jama’a domin kawo gyara da mafita cikin wannan lamarin ta yadda za a samu gaskiya da adalci kan kudaden da suke shigowa domin inganta tattalin arzikin kasa.

“Ta’asar masu hako ma’adinai ba bisa ka’ida na gurgunta ci gaban da ake samu a bangaren ma’adinai, kuma yana janyo lalata muhalli da gurbacewarsa wanda ke janyo asarar kudaden shiga masu tulin yawa da ya dace jama’an da ke yankunan da abun ya shafa da ma kasa su mora.”

A fadin Jonathan, akwai bukatar a gaggauta daukan matakan da suak dace wajen dakile aniyar masu satar ma’adinai domin kyautata kudin shiga, kare jama’a da kuma tabbatar da duk masu hakar ma’adinai na bin dokokin kasa.

Shi kuma, shugaban sojojin Nijeriya, Janaral Christopher Musa, ya ce masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba suna samun goyon baya daga wasu fitattun mutane da suke ba su kariya.

Da yake bude taron jin bahasin jama’an, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, wanda ya samu wakilcin Farfesa Julius Ihonbbere, ya lura kan cewa satar ma’adinai na ruguza tattalin arzikin kasar nan, lamarin da a cewarsa yake kara jefa jama’a cikin fatara da talauci, musamman manoman da suka dogara da noma amma aka lalata musu muhallin da suke zama da sunan hakar ma’adinai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakar Ma'adanaiMa’adanai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

Next Post

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

3 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

7 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

9 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

9 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

12 hours ago
Next Post
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma'aikatar Kiwo

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.