• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin majalisar wakilai kan albartun kasa, ya ce Nijeriya tana tafka asarar naira biliyan 9 a kowace shekara sakamakon aikace-aikacen masu hakar ma’adinai ta haramtattun hanyoyi a Nijeriya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rundunar sojin Nijeriya ta ce, ta cafke wadanda take zargi da hannu a hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba su 387 a cikin watanni bakwai da suka gabata.

  • Ramin Haƙar Ma’adanai Ya Rufta Da Mutum 3 A Jihar Neja
  • Miyar Agushi Mai Dadi Irin Ta Yammacin Nijeriya

Shugaban kwamitin majalisar, Jonathan Gaza Gbefwi, shi ne ya shaida hakan a yayin taron jin bahasin jama’a da kwamitin ya shirya kan binciken lamuran da suka shafi hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da na albartun kasa. Ya ce, wannan mummunar ayyukan satar ma’adinai ya janyo takaituwar jin gajiyar albartun da jama’an kasa ba su yi yadda ya dace.

Ya koka kan cewa zallar kaso uku kawai cikin kamfanonin da ke hakar ma’adinai ne suka biya na kudin lasisi hakar ma’adinai a kasar nan.

A cewarsa, daga cikin illar da hako ma’adinai ta barauniyar hanya ke janyowa har da janyo matsalolin tsaro da kuma arangama kan wake ko su waye masu ikon jan ragamar wuraren hako ma’adinai da albartun da ke ciki.

Labarai Masu Nasaba

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Ya ce, irin wannan rigimar na fantsama har ya shafi siyasa da zamantakewar jama’an da ke yankunan da abun ya shafa, wanda hakan ba daidai ba ne sam.

Sannan ya kara da cewa taron jin bahasin an shirya ne da zimmar shawo kan matsalolin da suke tattare da aikace-aikacen hako ma’adinai da kuma inganta hanyoyin samar da lasisi domin kyautata samar wa kasar nan da kudaden shiga da kuma cin gajiyar ma’adinan da suke jibge a kasar ba tare da wasu matsaloli ba.

“Nijeriya tana rasa naira biliyan 9 a kowace shekara kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba. Don haka, jagorancin majalisar wakilai ta 10 ya ga dacewar ya ji bahasin jama’a domin kawo gyara da mafita cikin wannan lamarin ta yadda za a samu gaskiya da adalci kan kudaden da suke shigowa domin inganta tattalin arzikin kasa.

“Ta’asar masu hako ma’adinai ba bisa ka’ida na gurgunta ci gaban da ake samu a bangaren ma’adinai, kuma yana janyo lalata muhalli da gurbacewarsa wanda ke janyo asarar kudaden shiga masu tulin yawa da ya dace jama’an da ke yankunan da abun ya shafa da ma kasa su mora.”

A fadin Jonathan, akwai bukatar a gaggauta daukan matakan da suak dace wajen dakile aniyar masu satar ma’adinai domin kyautata kudin shiga, kare jama’a da kuma tabbatar da duk masu hakar ma’adinai na bin dokokin kasa.

Shi kuma, shugaban sojojin Nijeriya, Janaral Christopher Musa, ya ce masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba suna samun goyon baya daga wasu fitattun mutane da suke ba su kariya.

Da yake bude taron jin bahasin jama’an, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, wanda ya samu wakilcin Farfesa Julius Ihonbbere, ya lura kan cewa satar ma’adinai na ruguza tattalin arzikin kasar nan, lamarin da a cewarsa yake kara jefa jama’a cikin fatara da talauci, musamman manoman da suka dogara da noma amma aka lalata musu muhallin da suke zama da sunan hakar ma’adinai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakar Ma'adanaiMa’adanai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

Next Post

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Related

Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

19 minutes ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 hours ago
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

5 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

7 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

9 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

10 hours ago
Next Post
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma'aikatar Kiwo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.