• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Nijeriya

Kwamitin majalisar wakilai kan albartun kasa, ya ce Nijeriya tana tafka asarar naira biliyan 9 a kowace shekara sakamakon aikace-aikacen masu hakar ma’adinai ta haramtattun hanyoyi a Nijeriya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rundunar sojin Nijeriya ta ce, ta cafke wadanda take zargi da hannu a hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba su 387 a cikin watanni bakwai da suka gabata.

  • Ramin Haƙar Ma’adanai Ya Rufta Da Mutum 3 A Jihar Neja
  • Miyar Agushi Mai Dadi Irin Ta Yammacin Nijeriya

Shugaban kwamitin majalisar, Jonathan Gaza Gbefwi, shi ne ya shaida hakan a yayin taron jin bahasin jama’a da kwamitin ya shirya kan binciken lamuran da suka shafi hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da na albartun kasa. Ya ce, wannan mummunar ayyukan satar ma’adinai ya janyo takaituwar jin gajiyar albartun da jama’an kasa ba su yi yadda ya dace.

Ya koka kan cewa zallar kaso uku kawai cikin kamfanonin da ke hakar ma’adinai ne suka biya na kudin lasisi hakar ma’adinai a kasar nan.

A cewarsa, daga cikin illar da hako ma’adinai ta barauniyar hanya ke janyowa har da janyo matsalolin tsaro da kuma arangama kan wake ko su waye masu ikon jan ragamar wuraren hako ma’adinai da albartun da ke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Ya ce, irin wannan rigimar na fantsama har ya shafi siyasa da zamantakewar jama’an da ke yankunan da abun ya shafa, wanda hakan ba daidai ba ne sam.

Sannan ya kara da cewa taron jin bahasin an shirya ne da zimmar shawo kan matsalolin da suke tattare da aikace-aikacen hako ma’adinai da kuma inganta hanyoyin samar da lasisi domin kyautata samar wa kasar nan da kudaden shiga da kuma cin gajiyar ma’adinan da suke jibge a kasar ba tare da wasu matsaloli ba.

“Nijeriya tana rasa naira biliyan 9 a kowace shekara kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba. Don haka, jagorancin majalisar wakilai ta 10 ya ga dacewar ya ji bahasin jama’a domin kawo gyara da mafita cikin wannan lamarin ta yadda za a samu gaskiya da adalci kan kudaden da suke shigowa domin inganta tattalin arzikin kasa.

“Ta’asar masu hako ma’adinai ba bisa ka’ida na gurgunta ci gaban da ake samu a bangaren ma’adinai, kuma yana janyo lalata muhalli da gurbacewarsa wanda ke janyo asarar kudaden shiga masu tulin yawa da ya dace jama’an da ke yankunan da abun ya shafa da ma kasa su mora.”

A fadin Jonathan, akwai bukatar a gaggauta daukan matakan da suak dace wajen dakile aniyar masu satar ma’adinai domin kyautata kudin shiga, kare jama’a da kuma tabbatar da duk masu hakar ma’adinai na bin dokokin kasa.

Shi kuma, shugaban sojojin Nijeriya, Janaral Christopher Musa, ya ce masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba suna samun goyon baya daga wasu fitattun mutane da suke ba su kariya.

Da yake bude taron jin bahasin jama’an, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, wanda ya samu wakilcin Farfesa Julius Ihonbbere, ya lura kan cewa satar ma’adinai na ruguza tattalin arzikin kasar nan, lamarin da a cewarsa yake kara jefa jama’a cikin fatara da talauci, musamman manoman da suka dogara da noma amma aka lalata musu muhallin da suke zama da sunan hakar ma’adinai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Next Post
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma'aikatar Kiwo

LABARAI MASU NASABA

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.