• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Jirgin Kasan Kaduna-Abuja: Gwamnatin Neja Ta Bukaci A Saki Matar Tsohon Gwamnan Kano Da ‘Ya’ya 5

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin Neja

Gwamnatin jihar Neja ta yunkuro domin tabbatar da an ceto mata da ‘ya’yan tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jigo a jam’iyyar APC, Janar Idris Garba daga hannun masu garkuwa da mutane wadanda harin Jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya shafa.

An sace matar tsohon gwamnan Maryam Bobbo, da ‘ya’yansa maza Abubakar da Ibrahim Idris Garba da kuma ‘ya’yansa uku Fatima, Imran da Zainab duk an yi garkuwa da su.

  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai
  • An Dakatar Da Sarkin Da Ya Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara

Sakataren Gwamnatin jihar Neja, Ahmed Ibrahim Matane, ne ya jagoranci tawagar gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello zuwa gidan tsohon gwamnan Kano, Wazirin Lapai kuma shugaban Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida a karshen mako.

Da ya ke misalta lamarin a matsayin abun tir da kaico na yin garkuwa da iyalansa har mutum shida, ya ce, harin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya sake farkar da gwamantin Neja kan yaki da ‘yan ta’adda.

Ya roki iyalan Wazirin Lapai da sauran wadanda aka yi garkuwa da ahalinsu da su ji kwarin guiwa daga bangaren gwamnati na cewa ita gwamnatin za ta yi dukkanin mai yiyuwa wajen ganin iyalansu sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Ya fada wa shugaban IBBU wakilan gwamnatin Neja, sun ziyarci gidansa ne domin tabbatar masa da cewa gwamantin jihar a kan kafafunta take wajen yaki da ‘yan ta’adda da tabbatar da cafke su a kowane lokaci.

Matane ya ce, “Shi (gwamna) ya umarci dukkanin hukumomin tsaro da su gaggauta daukan matakan ceto wadanda aka yi garkuwa da su, kuma da izinin Allah za su kubuta”.

“Mu gwamnati ne da muka san nauyin da ke kanmu kuma muna tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’ummar mu a kowani lokaci.”

Ya gargadi wadanda ke da hannu a aikace-aikacen ta’addanci da su fa sani gwamnati ba za ta taba barinsu suna cin karensu babu babbaka ba, don haka abun da ya fi musu kawai su gaggauta sauya matsayarsu su zama mutane ne kwarai.

Dukkanin wadanda suka yi magana a yayin ziyarar sun ce garkuwan da aka yi da iyalansu ya hanasu barci da sakewana kowani lokaci, sun roki gwamnati da ta yi duk mai yiyuwa wajen ceto wadanda aka yi garkuwa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa
Manyan Labarai

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Next Post
CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023

CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

October 24, 2025
Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

October 24, 2025
Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

October 24, 2025
Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.