• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Ba Gaskiya Ba Ne Cewar Muna Kashe Biliyan 196.9 Ga Masu Juna Biyu – Badaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan tsaro Muhammad Abubakar Badaru, ya umarci jami’an tsaro da su gabatar da jadawali da abubuwan da ake bukata domin kawo karshen kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan. 

Kazalika, ya ce, harkar tsaron kasar nan za ta bunkasa a cikin shekara daya.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?
  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

Badaru ya bayyana hakan ne a shalkwatar ma’aikatar tsaro a yayin da ya kama aiki a matsayin sabon ministan tsaro.

Ya ce, aikinsa da na karamin ministan tsaro da kuma aikin manyan jami’in tsaro, na cikin tsaka mai wuya idan har ba mu iya kawo karshen kalubalen rashin tsaro a cikin shekara daya ba.

A cewarsa, harkar tsaron a zamansa na ministan za ta bunkasa a daukacin fadin kasar nan a cikin shekara daya.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ya ci gaba da cewa, ba mu da wata hujja ta gazawa a kan nauyin da shugaban kasa ya dora mana, inda ya ce, za mu yi iya kokarinmu wajen tsamo kasar nan daga kalubalen rashin tsaro.

Ya kara da cewa, a matsayinmu na ‘yan siyasa ba za mu jurewa gazawa ba, domin zai yi wuya a ce mun gaza, domin ba za mu yadda da gazawa a wannan lokacin ba.

Bugu da kari, Badaru ya yi alkawarin hada kai da daukacin manyan jami’an tsaro a duk wata, domin a hada karfi da karfe wajen kawo karshen kalubalen rashin a kasar nan.

“Na aminta da daukacin matakan da karamin ministan tsaro ya bayyana, amma a nawa bangaren a yau shi ne za kara jaddada kokarinmu da kuma daukar alkawarin cewa, za mu samar da sauyi a fasalin harkar tsaro na kasar nan.”

Kazalika ya ce, “Zamu kuma bai wa daukacin hukumomin tsaro na kasar nan hadin kai kuma nan ba da jimawa ba, za mu fara gudanar da ganawa da hukumomin tsaro a duk wata bisa nufin lalubo da mafita a kan kalubalen rashin tsaro a kasar nan.”

“Mun yi sa’a shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kansa ya nada manyan jami’an tsaron kuma ya nada mu a matsayin ministocinsa.”

Bugu da kari, ya yi alkawarin yin nazari a kan rahotannin kalubalen rashin tsaro na kasar nan domin a fito da dabarun yadda za a kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ya ce, rahotannin na kalubalen rashin tsaron, na nan a ajiye wadanda za su ba mu damar daukar matakan da suka kamata don lalubo da mafita kan matsalar.

A na sa jawabin Hafsan rundunar tsaro Janar Christopher Musa, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya a fadin kasar nan, inda kuma ya yi fatan yaran da ke a kasar nan, za su girma a cikin yanayi na tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruMatsalar Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

Next Post

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

1 hour ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

3 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

5 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

8 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.