• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Ba Gaskiya Ba Ne Cewar Muna Kashe Biliyan 196.9 Ga Masu Juna Biyu – Badaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan tsaro Muhammad Abubakar Badaru, ya umarci jami’an tsaro da su gabatar da jadawali da abubuwan da ake bukata domin kawo karshen kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan. 

Kazalika, ya ce, harkar tsaron kasar nan za ta bunkasa a cikin shekara daya.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?
  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

Badaru ya bayyana hakan ne a shalkwatar ma’aikatar tsaro a yayin da ya kama aiki a matsayin sabon ministan tsaro.

Ya ce, aikinsa da na karamin ministan tsaro da kuma aikin manyan jami’in tsaro, na cikin tsaka mai wuya idan har ba mu iya kawo karshen kalubalen rashin tsaro a cikin shekara daya ba.

A cewarsa, harkar tsaron a zamansa na ministan za ta bunkasa a daukacin fadin kasar nan a cikin shekara daya.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

Ya ci gaba da cewa, ba mu da wata hujja ta gazawa a kan nauyin da shugaban kasa ya dora mana, inda ya ce, za mu yi iya kokarinmu wajen tsamo kasar nan daga kalubalen rashin tsaro.

Ya kara da cewa, a matsayinmu na ‘yan siyasa ba za mu jurewa gazawa ba, domin zai yi wuya a ce mun gaza, domin ba za mu yadda da gazawa a wannan lokacin ba.

Bugu da kari, Badaru ya yi alkawarin hada kai da daukacin manyan jami’an tsaro a duk wata, domin a hada karfi da karfe wajen kawo karshen kalubalen rashin a kasar nan.

“Na aminta da daukacin matakan da karamin ministan tsaro ya bayyana, amma a nawa bangaren a yau shi ne za kara jaddada kokarinmu da kuma daukar alkawarin cewa, za mu samar da sauyi a fasalin harkar tsaro na kasar nan.”

Kazalika ya ce, “Zamu kuma bai wa daukacin hukumomin tsaro na kasar nan hadin kai kuma nan ba da jimawa ba, za mu fara gudanar da ganawa da hukumomin tsaro a duk wata bisa nufin lalubo da mafita a kan kalubalen rashin tsaro a kasar nan.”

“Mun yi sa’a shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kansa ya nada manyan jami’an tsaron kuma ya nada mu a matsayin ministocinsa.”

Bugu da kari, ya yi alkawarin yin nazari a kan rahotannin kalubalen rashin tsaro na kasar nan domin a fito da dabarun yadda za a kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ya ce, rahotannin na kalubalen rashin tsaron, na nan a ajiye wadanda za su ba mu damar daukar matakan da suka kamata don lalubo da mafita kan matsalar.

A na sa jawabin Hafsan rundunar tsaro Janar Christopher Musa, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya a fadin kasar nan, inda kuma ya yi fatan yaran da ke a kasar nan, za su girma a cikin yanayi na tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruMatsalar Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

Next Post

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

Related

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

6 minutes ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

3 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

3 hours ago
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

7 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

16 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

17 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.