• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hawayen Munafurci

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Hawayen munafurci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka musulmi a sassan duniya na cikin watan Ramadan mai tsarki. A daidai wannan lokaci, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya fitar da sanarwa a kwanan baya, inda ya yi wa al’ummar musulmi gaisuwar watan Ramadan, tare da bayyana cewa, “musulmai ‘yan kabilar Uygur a jihar Xinjiang ta kasar Sin, da ‘yan kabilar Rohingya na kasashen Myanmar da Bangladesh, da Palesdinawa na zirin Gaza, suna fama da rikice-rikice da wahala.”

Ba wani abu da ya fi “hawayen munafurci” dacewa da siffanta wannan sanarwar da Mr.Blinken ya bayar, sabo da tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, duk da tsanantar yanayin jin kai a zirin Gaza, Amurka ta yi ta rura wutar rikicin, a sa’i da kuma take “kuka”.

  • Xi Ya Jajantawa Takwaransa Na Rasha Game Da Harin Ta’addanci Da Ya Auku A Moscow Oblast
  • Ba Za Mu Lamunci Amfani Da Yunwa A Matsayin Makamin Yaki A Gaza Ba – Tarayyar Turai

Kasancewarta babbar kawar Isra’ila da ma kasar da ta fi samar mata makamai, tun bayan barkewar rikicin, Amurka ta yi ta kara samar da gudummawar soja ga Isra’ila. Bisa rahoton da kafofin yada labarai na kasar ta Amurka suka bayar, an ce, ya zuwa yanzu, gwamnatin Biden ta sayar da makaman soja fiye da sau 100 a asirce ga Isra’ila, ciki har da makamai sama da dubu 10, matakin da ya sa masana’antun samar da makamai da ma masu ruwa da tsaki na kasar suka ci kazamar riba. Duk da mummunan yanayin jin kai da ake ciki a Gaza, sau hudu Amurka ta na jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da kudurin da aka gabatar ga kwamitin sulhu na MDD dangane da tsagaita bude wuta a zirin Gaza. Sai kuma a kwanakin baya, ita Amurka din ta gabatar da wani daftarin kuduri ga kwamitin sulhu dangane da batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza, amma a maimakon ta ce a tsagaita bude wuta nan da nan, sai ta gindaya sharuda ga tsagaita bude wuta, wanda ya saba wa daidaiton da akasarin mambobin kwamitin sulhun suka cimma, don haka, ba a kai ga zartas da shi ba.

Amma ga shi yanzu, Mr.Blinken ya fara damuwa da yanayin da Palasdinawa a zirin Gaza ke ciki, shin da gaske ne ya damu? Ba shakka ba haka ba ne, sabo da a kafin ya ambaci Pasdinawa, Mr.Blinken ya fara ne da ambaton “musulmai ‘yan kabilar Uygur a jihar Xinjiang ta kasar Sin”, lallai ainihin burinsa ke nan ya fake da sunan kulawa da yanayin da Palasdinawa a zirin Gaza ke ciki da ma hakkin musulmi don dakile kasar Sin ta hanyar amfani da wai yanayin da ‘yan kabilar Uygur ke ciki a jihar Xinjiang.

Amma karya fure take ba ta ‘ya’ya, duk wadanda suka taba zuwa jihar Xinjiang, ciki har da masana na kasashen yamma da ‘yan jarida da jakadu na kasashen musulmi dake kasar Sin, sun gano cewa, ana samun zaman lafiya da bunkasuwar tattalin arziki da zaman jituwa a tsakanin mabiya addinai daban daban a yankin Xinjiang na kasar Sin, kuma ana tabbatar da hakkin dan Adam na daukacin jama’a, ciki har da ‘yan kabilar Uygur. A hakika, babu rikici a yankin Xinjiang na kasar Sin, zirin Gaza ne ke fuskantar rikice-rikice. Haka kuma musulmai na yankin Xinjiang ba sa fama da yunwa ko kisa, amma miliyoyin musulmai na zirin Gaza suna fama da wadannan matsaloli.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Sama da kwanaki 160 ke nan tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda ya sa fararen hula sama da dubu 32 suka rasa rayukansu, baya ga miliyoyin dake fama da yunwa. Kamata ya yi Amurka ta daina wasan siyasa da yanayin jin kai na zirin Gaza. Abin da ya kamata ta yi shi ne ta dauki hakikanan matakai na ceton rayukan musulmai a Gaza, a maimakon ta fitar da sanarwa maras ma’ana.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yansanda Sun Kama Mutum 6 Bisa Zargin Satar Keke-napep Uku A Adamawa

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Tarwatsa Wasu Kungiyoyin Ta’ammuli Da Hodar Iblis A Abuja Da Kano

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

3 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

3 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

4 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

5 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

6 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

6 days ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

Hukumar NDLEA Ta Tarwatsa Wasu Kungiyoyin Ta'ammuli Da Hodar Iblis A Abuja Da Kano

LABARAI MASU NASABA

'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Hawayen munafurci

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.