ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hawayen Munafurci

by CGTN Hausa
2 years ago
Hawayen munafurci

Yanzu haka musulmi a sassan duniya na cikin watan Ramadan mai tsarki. A daidai wannan lokaci, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya fitar da sanarwa a kwanan baya, inda ya yi wa al’ummar musulmi gaisuwar watan Ramadan, tare da bayyana cewa, “musulmai ‘yan kabilar Uygur a jihar Xinjiang ta kasar Sin, da ‘yan kabilar Rohingya na kasashen Myanmar da Bangladesh, da Palesdinawa na zirin Gaza, suna fama da rikice-rikice da wahala.”

Ba wani abu da ya fi “hawayen munafurci” dacewa da siffanta wannan sanarwar da Mr.Blinken ya bayar, sabo da tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, duk da tsanantar yanayin jin kai a zirin Gaza, Amurka ta yi ta rura wutar rikicin, a sa’i da kuma take “kuka”.

  • Xi Ya Jajantawa Takwaransa Na Rasha Game Da Harin Ta’addanci Da Ya Auku A Moscow Oblast
  • Ba Za Mu Lamunci Amfani Da Yunwa A Matsayin Makamin Yaki A Gaza Ba – Tarayyar Turai

Kasancewarta babbar kawar Isra’ila da ma kasar da ta fi samar mata makamai, tun bayan barkewar rikicin, Amurka ta yi ta kara samar da gudummawar soja ga Isra’ila. Bisa rahoton da kafofin yada labarai na kasar ta Amurka suka bayar, an ce, ya zuwa yanzu, gwamnatin Biden ta sayar da makaman soja fiye da sau 100 a asirce ga Isra’ila, ciki har da makamai sama da dubu 10, matakin da ya sa masana’antun samar da makamai da ma masu ruwa da tsaki na kasar suka ci kazamar riba. Duk da mummunan yanayin jin kai da ake ciki a Gaza, sau hudu Amurka ta na jefa kuri’ar nuna rashin amincewa da kudurin da aka gabatar ga kwamitin sulhu na MDD dangane da tsagaita bude wuta a zirin Gaza. Sai kuma a kwanakin baya, ita Amurka din ta gabatar da wani daftarin kuduri ga kwamitin sulhu dangane da batun tsagaita bude wuta a zirin Gaza, amma a maimakon ta ce a tsagaita bude wuta nan da nan, sai ta gindaya sharuda ga tsagaita bude wuta, wanda ya saba wa daidaiton da akasarin mambobin kwamitin sulhun suka cimma, don haka, ba a kai ga zartas da shi ba.

ADVERTISEMENT

Amma ga shi yanzu, Mr.Blinken ya fara damuwa da yanayin da Palasdinawa a zirin Gaza ke ciki, shin da gaske ne ya damu? Ba shakka ba haka ba ne, sabo da a kafin ya ambaci Pasdinawa, Mr.Blinken ya fara ne da ambaton “musulmai ‘yan kabilar Uygur a jihar Xinjiang ta kasar Sin”, lallai ainihin burinsa ke nan ya fake da sunan kulawa da yanayin da Palasdinawa a zirin Gaza ke ciki da ma hakkin musulmi don dakile kasar Sin ta hanyar amfani da wai yanayin da ‘yan kabilar Uygur ke ciki a jihar Xinjiang.

Amma karya fure take ba ta ‘ya’ya, duk wadanda suka taba zuwa jihar Xinjiang, ciki har da masana na kasashen yamma da ‘yan jarida da jakadu na kasashen musulmi dake kasar Sin, sun gano cewa, ana samun zaman lafiya da bunkasuwar tattalin arziki da zaman jituwa a tsakanin mabiya addinai daban daban a yankin Xinjiang na kasar Sin, kuma ana tabbatar da hakkin dan Adam na daukacin jama’a, ciki har da ‘yan kabilar Uygur. A hakika, babu rikici a yankin Xinjiang na kasar Sin, zirin Gaza ne ke fuskantar rikice-rikice. Haka kuma musulmai na yankin Xinjiang ba sa fama da yunwa ko kisa, amma miliyoyin musulmai na zirin Gaza suna fama da wadannan matsaloli.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Sama da kwanaki 160 ke nan tun bayan barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda ya sa fararen hula sama da dubu 32 suka rasa rayukansu, baya ga miliyoyin dake fama da yunwa. Kamata ya yi Amurka ta daina wasan siyasa da yanayin jin kai na zirin Gaza. Abin da ya kamata ta yi shi ne ta dauki hakikanan matakai na ceton rayukan musulmai a Gaza, a maimakon ta fitar da sanarwa maras ma’ana.

 

Hawayen munafurci
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

Hukumar NDLEA Ta Tarwatsa Wasu Kungiyoyin Ta'ammuli Da Hodar Iblis A Abuja Da Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.