• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Gidan Yarin Kuje Ta Tabbatar Da Mutuwar Fursuna A Gidan Yarin Kuje

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kuje

Hukumar Kula da Gidajen Yari, ta tabbatar da cewa wani fursuna guda daya ya rasu a gidan yarin Kuje sakamakon fama da rashin lafiya.

Kwanturolan hukumar na birnin tarayya, Ahmed Musa Ahmed, ne ya tabbatar da mutuwar fursunan, yana mai mika jajensa da ta’aziyyar ga ahalin mamacin bisa rashin da suka yin.

  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u
  • Kotu Ta Sake Hana Ba Da Belin Abba Kyari

Ya nanata aniyar hukumar na ci gaba da mayar da hankali sosai wajen kula da lafiyar fursunoni da kuma ma’aikatan gidan yari a kowane lokaci.

A wata sanarwar da kakakin hukumar na Abuja, Chukwuedo Humphrey, ya fitar, ya ce fursunan ya mutu ne bayan fama da rashin lafiya, kuma an masa jinyar wasu cututtuka yadda ya kamata.

Ahmed, ya shawarci fursunonin da suke kan amsar wasu magunanna musamman da suke fitowa su fada musu domin fuskantar cututtukan da ke damunsu a kowane lokaci tun da magunguna suna nan kuma kyauta ake basu.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Sanarwar ta kara da cewa, “Cikin gaggawa an dora mamacin kan samun kulawar magani ta musamman kafin rasuwarsa har ma sai da ta kai an sauya masa wurin jinya zuwa asibitin koyarwa  a Jami’ar Abuja da ke Gwagwalada domin samun kulawar likitoci yadda ya kamata.

“Abun takaici, a lokacin da jikin mamacin ya tsananta a karshen mako, duk kokarin da likitoci suka yi domin ceto rayuwarsa abun ya ci tura kwanansa ya kare.”

Ya ce an shirya wa mamacin addu’a ta musamman a gidan yarin domin nema masa salama.

Kazalika wasu ma’aikatan gidan yari da suka zanta da LEADERSHIP sun zargi rashin kula daga hukumar kula da gidajen yarin.

Ma’aikatan da suka nemi a sakaya sunansu, sun ce kalubalen matsalar ingancin kayan kula da lafiyar fursunoni na daga cikin manyan matsalolin da suke addabar gidan yarin.

Sun kuma yi zargin cewa wanda ya mutu bai samu kulawar da ta dace ba tun lokacin da ya fara jinya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.