• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Gidan Yarin Kuje Ta Tabbatar Da Mutuwar Fursuna A Gidan Yarin Kuje

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Hukumar Gidan Yarin Kuje Ta Tabbatar Da Mutuwar Fursuna A Gidan Yarin Kuje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Gidajen Yari, ta tabbatar da cewa wani fursuna guda daya ya rasu a gidan yarin Kuje sakamakon fama da rashin lafiya.

Kwanturolan hukumar na birnin tarayya, Ahmed Musa Ahmed, ne ya tabbatar da mutuwar fursunan, yana mai mika jajensa da ta’aziyyar ga ahalin mamacin bisa rashin da suka yin.

  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u
  • Kotu Ta Sake Hana Ba Da Belin Abba Kyari

Ya nanata aniyar hukumar na ci gaba da mayar da hankali sosai wajen kula da lafiyar fursunoni da kuma ma’aikatan gidan yari a kowane lokaci.

A wata sanarwar da kakakin hukumar na Abuja, Chukwuedo Humphrey, ya fitar, ya ce fursunan ya mutu ne bayan fama da rashin lafiya, kuma an masa jinyar wasu cututtuka yadda ya kamata.

Ahmed, ya shawarci fursunonin da suke kan amsar wasu magunanna musamman da suke fitowa su fada musu domin fuskantar cututtukan da ke damunsu a kowane lokaci tun da magunguna suna nan kuma kyauta ake basu.

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanarwar ta kara da cewa, “Cikin gaggawa an dora mamacin kan samun kulawar magani ta musamman kafin rasuwarsa har ma sai da ta kai an sauya masa wurin jinya zuwa asibitin koyarwa  a Jami’ar Abuja da ke Gwagwalada domin samun kulawar likitoci yadda ya kamata.

“Abun takaici, a lokacin da jikin mamacin ya tsananta a karshen mako, duk kokarin da likitoci suka yi domin ceto rayuwarsa abun ya ci tura kwanansa ya kare.”

Ya ce an shirya wa mamacin addu’a ta musamman a gidan yarin domin nema masa salama.

Kazalika wasu ma’aikatan gidan yari da suka zanta da LEADERSHIP sun zargi rashin kula daga hukumar kula da gidajen yarin.

Ma’aikatan da suka nemi a sakaya sunansu, sun ce kalubalen matsalar ingancin kayan kula da lafiyar fursunoni na daga cikin manyan matsalolin da suke addabar gidan yarin.

Sun kuma yi zargin cewa wanda ya mutu bai samu kulawar da ta dace ba tun lokacin da ya fara jinya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaFursunaGidan Yarin KujeKulawaLikitociMaganiRashin Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kogi Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Bayan Rasuwar Mutane 2

Next Post

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

40 minutes ago
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
Labarai

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

2 hours ago
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

4 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

8 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

9 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

10 hours ago
Next Post
Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.