ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
11 months ago
Knarda

Hukumar Bunkasa Aikin Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA), ta horar da manoman Wake tare da ba su kayan aiki; don kara habaka nomansu.

Manoman da suka amfana da horon, sun bayyana jin dadinsu musamman ta fuskar ba su sabon Irin Wake da aka yi; domin amfanuwarsu.

  • Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500
  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Manajan Darakta na Hukumar ta KNARDA, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana cewa, Hukumar tasa a karkashin shirin aikin bunkasa aikin noma da Bankin Musulunci na Bunkasa Aikin na Noma (IsDB), tare da tallafin Shirin Inganta Rayuwar Alumma (LLF) ne suka zuba kudede tare da raba wa manoman sabon Irin na Wake.

ADVERTISEMENT

Kurawa ya sanar da cewa, an raba wa manoman Irin ne, domin kara habaka noman Wake da kuma bunkasa girbinsa a jihar.

Manajan ya bayyana haka ne, a jawabinsa yayin samar da wannan dauki a kauyen Riga Fada da ke Karamar Hukumar Kumbotso a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

A cewar Kurawan, an samu nasarori da dama a karkashin wannan aiki, inda ya kara da cewa, kamar sauran sassan Nijeriya; su ma manoman da ke Jihar Kano, sun samu bayanai; musamman a kan noman rani.

Shi ma a nasa jawabin, wani jami’i a hukumar ta KNARDA Muhammad Ahmad Nahannu ya bayyana cewa, sabon Irin Waken; na samar da girbi mai yawa fiye da Irin Waken da manoman suka saba shukawa, wanda ya kai kashi goma na rubun da ake samu a girbin.

Ahmad ya kara da cewa, sama da rukunin al’umma 258 da suka hada da mata 25 daga kowanne cikin rukuni, sun amfana da wannan tallafi daban-daban na wannan aiki.

Shi kuwa, Ko’odinetan aikin na KSADP a Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba ya bayyana cewa, Gwamnati ce ke taimaka wa aikin, musamman don kara habaka fannin aikin noma ta hanyar bayar da tallafin kayan aikin noma, bayar da rancen noma, sama wa manoma kasuwa da sauran makamantansu.

Daya daga cikin manoman da suka amfana da tallafin, Malam Auwal Isah Kumbotso ya bayyna cewa, bisa wannan ci gaba da aka sama musu a karkashin wannan aiki, nan ba da jimawa ba; Jihar Kano za ta zama cibiyar noman Wake.

Kumbotso ya kara da cewa, bisa wannan mayar da hankali da aka yi, hakan ya nuna cewa, gwamnatin jihar za a kara nuna sha’awa a aikin noma fiye da yadda ake da sha’awarsa a baya.

A cewarsa,“Mun gamsu da sabon Irin Waken da aka raba mana, domin Iri da aka yi gwajinsa, mahukunta sun aminta da shi”.

Ya kara da cewa, daukacin wadanda suka amfana da sabon Irin, mun tabbatar da hakan domin sakamakon da muka samu daga yin amfani da sabon Irin, mun gamsu da haka.

Ya sanar da cewa, a matsayina na manomi; zan iya bayar da shedar cewa, girbin da na yi na sabon Waken sau biyu; ya rubanya girbin da na yi a bara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

Bayan Rashin Nasara A Ballon d’Or, Vinícius Ya Lashe Wata Babbar Kyauta A Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.