• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
12 hours ago
in Labarai
0
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar hana fasa kwabri ta kasa reshen jihar Katsina ta yi nasarar kama kayan maye da motoci guda biyu wanda kudin ya kai naira miliyan 721,592,250 a Katsina.

Wannan nasara dai sun same ta a yankin Daura akan iyakar Nijeriya da kasar Nijar inda ake kokarin shigowa da wadannan haramtattu kayayyaki.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Da yake jawabi a lokacin taron manema labarai a Katsina shugaban hukumar Idris Abba Aji ya bayyana wannan nasara a matsayin ta kasa baki daya.

Ya kara da cewa irin wadannan kayayyakin maye ne ake kaiwa ‘yan ta’adda domin su ci gaba da kai wa al’umma hare-haren wuce gona da iri a jihar Katsina da arewacin Nijeriya baki daya.

Abba Aji wanda ya ce kama wadannan kayayyaki za su taimaka wa kokarin jami’an tsaro da gwamnati wajen ganin an kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya musamman yankin arewa da batun ya fi kamari.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Shugaban hukumar hana fasa kwabri ta kasa ya ce sun kama kwali goma sha hudu na Tramadol wanda kudin da ya kai naira miliyan 650 da kuma pregabalin kwali 38 wanda kudin da ya kai naira miliyan 28,500

Kazalika ya ci gaba bayanin cewa sun kama tabar wiwi wanda ya kai kulli 174 kudin ta sun kai naira miliyan 1,807,250 .

“Duk a lokacin wannan kamen mun samu nasarar kama motoci guda biyu Toyota land cruiser mai launi ash mai lamba ABJ 451 AP Abuja wanda kudin ta suka kai miliyan 10,509

Sai kuma Toyota Jeep land cruiser baka mai lamba YAB 935 BJ Abuja wanda suka ce kudin ta zai kai naira miliyan 12,600.

A cewar sa, sun kama wadannan motoci bisa bayanan sirri da suka samu wanda kuma sun cafke mutum guda wanda yanzu an ba da belin sa kafin ranar zuwa kotu.

Ya kara da cewa jama’a sun fara korafi a kan yadda jami’an tsaro na Kwastam ke tare manyan motoci a kan hanya wanda ya ce labarin sirri da suke samu ya sa suke yin haka wanda yanzu ga nasara an samu.

“Yanzu an fito da sabbin dabarun yin fasa kwabri inda ake amfani da manyan motoci Na alfarma wanda ake sa ran cewa ba za a iya tsaida su a kan hanya ba, sai a dauko kayan laifi a wuce da su,”inji shi

Idris Abba Aji ya ce jami’an da da sauran jami’an tsaro a shirye suke wajen ganin sun taimaka wa kokarin da gwamnati ke yi na dakile shigowa da muggan kwayoyi domin kaiwa ‘yan bindiga.

Kazalika ya nuna irin illar da shigowa da irin wadannan kwayoyi ke yi wajen ba da aiki baya musamman fada da ‘yan bindiga da mafi yawan su sai shi. Sha kwaya kafin su kai hare-haren wuce gona da iri.

Daga karshe ya yi fatan cewa al’umma su ci gaba da taimaka masu da bayanan sirri domin ganin an samu nasarar da ake bukata a Nijeriya da kuma jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Katsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Next Post

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

6 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

7 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

7 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

8 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

10 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

11 hours ago
Next Post
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da "Canji Mai Girma" Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.