• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
1 month ago
in Labarai
0
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar hana fasa kwabri ta kasa reshen jihar Katsina ta yi nasarar kama kayan maye da motoci guda biyu wanda kudin ya kai naira miliyan 721,592,250 a Katsina.

Wannan nasara dai sun same ta a yankin Daura akan iyakar Nijeriya da kasar Nijar inda ake kokarin shigowa da wadannan haramtattu kayayyaki.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Da yake jawabi a lokacin taron manema labarai a Katsina shugaban hukumar Idris Abba Aji ya bayyana wannan nasara a matsayin ta kasa baki daya.

Ya kara da cewa irin wadannan kayayyakin maye ne ake kaiwa ‘yan ta’adda domin su ci gaba da kai wa al’umma hare-haren wuce gona da iri a jihar Katsina da arewacin Nijeriya baki daya.

Abba Aji wanda ya ce kama wadannan kayayyaki za su taimaka wa kokarin jami’an tsaro da gwamnati wajen ganin an kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya musamman yankin arewa da batun ya fi kamari.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Shugaban hukumar hana fasa kwabri ta kasa ya ce sun kama kwali goma sha hudu na Tramadol wanda kudin da ya kai naira miliyan 650 da kuma pregabalin kwali 38 wanda kudin da ya kai naira miliyan 28,500

Kazalika ya ci gaba bayanin cewa sun kama tabar wiwi wanda ya kai kulli 174 kudin ta sun kai naira miliyan 1,807,250 .

“Duk a lokacin wannan kamen mun samu nasarar kama motoci guda biyu Toyota land cruiser mai launi ash mai lamba ABJ 451 AP Abuja wanda kudin ta suka kai miliyan 10,509

Sai kuma Toyota Jeep land cruiser baka mai lamba YAB 935 BJ Abuja wanda suka ce kudin ta zai kai naira miliyan 12,600.

A cewar sa, sun kama wadannan motoci bisa bayanan sirri da suka samu wanda kuma sun cafke mutum guda wanda yanzu an ba da belin sa kafin ranar zuwa kotu.

Ya kara da cewa jama’a sun fara korafi a kan yadda jami’an tsaro na Kwastam ke tare manyan motoci a kan hanya wanda ya ce labarin sirri da suke samu ya sa suke yin haka wanda yanzu ga nasara an samu.

“Yanzu an fito da sabbin dabarun yin fasa kwabri inda ake amfani da manyan motoci Na alfarma wanda ake sa ran cewa ba za a iya tsaida su a kan hanya ba, sai a dauko kayan laifi a wuce da su,”inji shi

Idris Abba Aji ya ce jami’an da da sauran jami’an tsaro a shirye suke wajen ganin sun taimaka wa kokarin da gwamnati ke yi na dakile shigowa da muggan kwayoyi domin kaiwa ‘yan bindiga.

Kazalika ya nuna irin illar da shigowa da irin wadannan kwayoyi ke yi wajen ba da aiki baya musamman fada da ‘yan bindiga da mafi yawan su sai shi. Sha kwaya kafin su kai hare-haren wuce gona da iri.

Daga karshe ya yi fatan cewa al’umma su ci gaba da taimaka masu da bayanan sirri domin ganin an samu nasarar da ake bukata a Nijeriya da kuma jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Katsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Next Post

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Related

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

26 minutes ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

1 hour ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

3 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da ÆŠansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

4 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da ÆŠansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

13 hours ago
Next Post
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da "Canji Mai Girma" Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi AlÆ™awarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi AlÆ™awarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.