• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Labarai
0
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta fara bin diddigin ayyukan mazabu na naira biliyan 21 a fadin Jihar Kaduna.

Hukumar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da ayyuka ga jama’a.

  • An Gano Buhunan Shinkafar Tallafi 16,800 Mai Nauyin Kilo 50 Da Aka Sauyawa Buhu A Kano
  • Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, babban sufeto na ICPC, Haruna Aminu, wanda ya wakilci sashen bin diddigi na mazaba da zartarwa a karkashin jagorancin shugaban ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu, ya ce hukumar na bibiyar ayyuka 60 a fadin Jihar Kaduna.

“Mun zo nan ne domin bin diddigin ayyuka kusan 60 a fadin Jihar Kaduna da adadin kudinsu ya kai naira biliyan 21. Mun fara ne a ranar Laraba a yankin Kafanchan, inda muka binciki akalla ayyuka 21. Yanzu haka muna babban garin Kaduna, Unguwar Kabala, muna mai da hankali kan ayyuka irin su fitulun titi mai amfani da hasken rana da aka saka a fadin garin.

“Gaba daya dai, a kan aikin hasken rana, mun ga matakin da ake kai na aiwatarwa, sannan kuma daga dayan kusurwar, mun sami damar gano wasu ayyukan. Wannan aiki ne da ya taba rayuwar mutane,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Ya kuma ce hukumar za ta ga yadda za ta tura dan kwangilar ya kammala aikin, inda ya nuna cewa babu wani dan kwangila da za a tsallake saboda ba zai yiwu ba su karbi kudin gwamnati su tafi ba tare da kammala ayyuka ba.

Ya ce zamanin watsi da ayyuka ya wuce domin an ba su dukkan umarni da goyon baya don tunkarar duk wadanda suka kasa kamala ayyukansu a kan lokaci.

Aminu ya bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kammala wasu ayyuka, musamman fitilun titi masu amfani da hasken rana ya kawo cikas ga tasirinsa ga al’umma.

“Wadannan ayyuka na da muhimmanci wajen inganta rayuwa a Jihar Kaduna. Idan aka kammala a shekarar da ta gabata kamar yadda aka tsara, da a yanzu za su kawo gagarumin sauyi,” in ji shi.

Ya ce mataki na gaba na wannan yunkuri zai kunshi dakushe ‘yan kwangilar da suka kasa gudanar da ayyukansu, da tabbatar da cewa ‘yan kasa sun samu ribar dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ICPCKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

Next Post

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

6 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

7 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

8 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

8 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

9 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

9 hours ago
Next Post
Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.