• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta fara bin diddigin ayyukan mazabu na naira biliyan 21 a fadin Jihar Kaduna.

Hukumar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da ayyuka ga jama’a.

  • An Gano Buhunan Shinkafar Tallafi 16,800 Mai Nauyin Kilo 50 Da Aka Sauyawa Buhu A Kano
  • Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, babban sufeto na ICPC, Haruna Aminu, wanda ya wakilci sashen bin diddigi na mazaba da zartarwa a karkashin jagorancin shugaban ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu, ya ce hukumar na bibiyar ayyuka 60 a fadin Jihar Kaduna.

“Mun zo nan ne domin bin diddigin ayyuka kusan 60 a fadin Jihar Kaduna da adadin kudinsu ya kai naira biliyan 21. Mun fara ne a ranar Laraba a yankin Kafanchan, inda muka binciki akalla ayyuka 21. Yanzu haka muna babban garin Kaduna, Unguwar Kabala, muna mai da hankali kan ayyuka irin su fitulun titi mai amfani da hasken rana da aka saka a fadin garin.

“Gaba daya dai, a kan aikin hasken rana, mun ga matakin da ake kai na aiwatarwa, sannan kuma daga dayan kusurwar, mun sami damar gano wasu ayyukan. Wannan aiki ne da ya taba rayuwar mutane,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Ya kuma ce hukumar za ta ga yadda za ta tura dan kwangilar ya kammala aikin, inda ya nuna cewa babu wani dan kwangila da za a tsallake saboda ba zai yiwu ba su karbi kudin gwamnati su tafi ba tare da kammala ayyuka ba.

Ya ce zamanin watsi da ayyuka ya wuce domin an ba su dukkan umarni da goyon baya don tunkarar duk wadanda suka kasa kamala ayyukansu a kan lokaci.

Aminu ya bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kammala wasu ayyuka, musamman fitilun titi masu amfani da hasken rana ya kawo cikas ga tasirinsa ga al’umma.

“Wadannan ayyuka na da muhimmanci wajen inganta rayuwa a Jihar Kaduna. Idan aka kammala a shekarar da ta gabata kamar yadda aka tsara, da a yanzu za su kawo gagarumin sauyi,” in ji shi.

Ya ce mataki na gaba na wannan yunkuri zai kunshi dakushe ‘yan kwangilar da suka kasa gudanar da ayyukansu, da tabbatar da cewa ‘yan kasa sun samu ribar dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ICPCKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

Next Post

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

22 minutes ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

3 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

4 hours ago
Kaduna
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

5 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

7 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

7 hours ago
Next Post
Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Kaduna

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.