• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Labarai
0
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta fara bin diddigin ayyukan mazabu na naira biliyan 21 a fadin Jihar Kaduna.

Hukumar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da ayyuka ga jama’a.

  • An Gano Buhunan Shinkafar Tallafi 16,800 Mai Nauyin Kilo 50 Da Aka Sauyawa Buhu A Kano
  • Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, babban sufeto na ICPC, Haruna Aminu, wanda ya wakilci sashen bin diddigi na mazaba da zartarwa a karkashin jagorancin shugaban ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu, ya ce hukumar na bibiyar ayyuka 60 a fadin Jihar Kaduna.

“Mun zo nan ne domin bin diddigin ayyuka kusan 60 a fadin Jihar Kaduna da adadin kudinsu ya kai naira biliyan 21. Mun fara ne a ranar Laraba a yankin Kafanchan, inda muka binciki akalla ayyuka 21. Yanzu haka muna babban garin Kaduna, Unguwar Kabala, muna mai da hankali kan ayyuka irin su fitulun titi mai amfani da hasken rana da aka saka a fadin garin.

“Gaba daya dai, a kan aikin hasken rana, mun ga matakin da ake kai na aiwatarwa, sannan kuma daga dayan kusurwar, mun sami damar gano wasu ayyukan. Wannan aiki ne da ya taba rayuwar mutane,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Ya kuma ce hukumar za ta ga yadda za ta tura dan kwangilar ya kammala aikin, inda ya nuna cewa babu wani dan kwangila da za a tsallake saboda ba zai yiwu ba su karbi kudin gwamnati su tafi ba tare da kammala ayyuka ba.

Ya ce zamanin watsi da ayyuka ya wuce domin an ba su dukkan umarni da goyon baya don tunkarar duk wadanda suka kasa kamala ayyukansu a kan lokaci.

Aminu ya bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kammala wasu ayyuka, musamman fitilun titi masu amfani da hasken rana ya kawo cikas ga tasirinsa ga al’umma.

“Wadannan ayyuka na da muhimmanci wajen inganta rayuwa a Jihar Kaduna. Idan aka kammala a shekarar da ta gabata kamar yadda aka tsara, da a yanzu za su kawo gagarumin sauyi,” in ji shi.

Ya ce mataki na gaba na wannan yunkuri zai kunshi dakushe ‘yan kwangilar da suka kasa gudanar da ayyukansu, da tabbatar da cewa ‘yan kasa sun samu ribar dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ICPCKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

Next Post

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

7 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

8 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

10 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

13 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

13 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

15 hours ago
Next Post
Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.