• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya

by Ra'ayinmu
1 month ago
in Labarai
0
Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da Nijeriya ke ci gaba da fuskantar dimbin matsalolin tattalin arziki da kuma kalubalen kare muhalli, wani sabon rahoto da aka fitar ya nuna cewa, ana kuma fargabar fuskantar matsalar karancin abinci a kasar, wadda kuma za ta iya jefa miliyoyin ‘yan kasar a cikin yunwa da rasashin samun abinci, mai gina jiki.

Wani rahoto na watan Fabirairu zuwa na Maris da masu fashin baki a CH suka fitar ya nuna cewa, daga watan Yuni zuwa na Agustan 2025, akalla ‘yan Nijeriya miliyan 30.6, cikinsu har da ‘yan gudun hijira a jihohin kasar 26 har da Abuja, za su iya fusakantar karancin abinci da kuma rashin samun abinci mai gina jiki.

  • Duk Da Dokar ‘Yancin Samar Da Abinci: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Ƙaranci Abinci A Nijeriya
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya

Adadin wannan alkaluman sun nuna cewa, an samu ‘yar raguwar da ta kai miliyan 33.1 a watan Nuwambar 2024, inda wannan lamarin ke da matukar bukatar masu ruwa da tsaki su smar da daukin gaggawa domin lalubo da mafita kan wannan matsalar.

Wannan rahoton ha hadaka a tsakanin Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci da kuma Hukumar Samar da Abinci da ke a Majalisar dinkin Duniya FAO tare da hadin guwair sauran abokan hadaka, sun yi dubi a kan yanayin karancin abinci da Nijeriya za ta iya fuskanta.

Kazalika, duba da yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasar, a wasu yankunan kasar ana ci gaba da fuskantar gaza samun iya cin abinci, saboda yadda a yankunan, ake ci gaba da fusnatar barazar rashin tsaro, kalubalen sauyin yanayi da kuma kalubalen sauye-sauyen tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

Jihohin da wannan matsalar ta fi shafa sun hada da, Zamfara, Borno, Yobe da kuma Katsina, musamman duba da yadda aukuwar yawan rikice-rikice, ya tarwatsa rayuwar miliyoyin alumomin yakin da fadawa cikin kangin fatara da yunwa da kuma rashin samun wadataccen abinci.

A ra’ayin mu, matsalar karancin abinci a kasar nan, ba boyayayen abu bane, musammamn duba da cewa, yawan aukuwar tashe-tashen hankula, kalubalen rashin tsaro da matsatin tattalin arziki, suna manyan hummulhaba’isin da ke janyo karancin abinci a a cikin alumma.

Misali, yawan samun hare-haren ‘yan bindiga a yankin kudu maso gabas, ayyukan ‘yan bindiga daji a yankin arewa masu yamma da kuma rikice-rikicen kabilanci a sauran yankuanan, sun janyo tarwatsa miliyoyin alumomi daga matsugunan su, lalata gonakansu wanda hakan ya janyo, aka samu raguwar noma amfanin gona, sauyar da amfanin gonar, inda hakan ya kuma haifar da karancin abinci a cikin alumma tare da samun hauhawan farashin kayan abinci.

Akasarin fannin noma a kasar nan, ya dogara ne kachokam kan samun ruwan damina, inda kuma fanin ke cin karo da samun sauyin yanayi, wanda hakan ke sanya wa a fusaknaci fari ko sauyin samun yanayin saukar ruwan sama da kuma akuwar annobar ambaliyar ruwan sama, inda hakan ke yiwa amfanin gona da aka shuka illa da kuma shafar dabbobi.

Wannan matsalar ta ambaliyar ruwansaman ba wai ta tsaya a kan amfanin gona bane, ta na kuma lalata matsunan alumma da kuma kara haifar da talauci a tsakanin su.

Sauye-sauye na dogon zango kan tattalin arziki da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su a shekarar 2024 ta kuma wanzar da su, sun kasance za su iya janyo nakasu, a yunkurin da ake yi na samar da wadataccen abinci a kasar nan.

Duba da yadda ake ci gaba da samun hauhawan farashin kaya, karyewar darajar Naira, samun karuwar farashin man fetur, hakan yakara haifar da tsadar noma amfanin gona, tsadar sufuri, wanda hakan zai kara sanya wa masu sayen kayan abincin, su saya da tsadar gaske.

Bugu da kari, matsain na tattalin arzikin ya kuma janyowa alumma rashin samun wasu abubuwa kamar na iya kula da kiwon lafiyarsu da ci gaba da daukar nauyin karatun ‘ya’yansu.

Hukumar FOA tare da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da sasshen samar da abinci na Majalisar dinkin Duniya wato WFP da Asusun tallafawa kanannan yara na Majalisar dinkin Duniya UNICEF, Gidanuniyar Kula da kananan Yara da kuma kungiyar Kare Raji ta Mercy Corps, sun jima suna jaddada mahimmancin daukar matakan gaggawa na jin kai kafin aukuwar dukkanin wata annoba.

Daga cikin sakamkon taro na CH da aka gudaanr a Abuja wakilin FOA Nijeriya Kouacoau Dominikue Koffy ya jabawa Gwamnatin Tarayya da kuma masu ruwa da tsaki a CH, musamman bisa mayar da hankali da suka yi wajen ganin an samar da wadataccen abinci da kuma sanya ido da suke yi don a samar da wadataccen abincin.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatocin Jihohi da sauran abokan hadaka da su zuba kudade domin a wanzar da tsarin na kasa da a za a gudanar a watan Okotobar 2025, inda ya yi nuni da cewa, ba tare da an samar da bayanai da samar da kyakyanwan shiri zai yi wuya, a cimma burin da aka sanya a gaba.

A ra’ayin wannan jaridar, mun yi amannar cewa, kalubalen karancin abinci abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe, wanda hakan zai wuce batun siyasantar da maganar da shelanta samar da Rumbunan adana hatsi.

Ya zama wajibi Gwamnatin Tarayya ta ayyana dokar ta baci wajen samar da wadataccen abinci tare da kafa tawaga mai karfi da za ta hada da Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomin Tsaro, kungiyoyin Jin kai, Kamfanonin Masu Zaman Kansu da sauran masu ruwa da tsaki, musamman domin a samar da tare da kaddamar da kyakyawan tsari na kasa.

Dole ne Gwamnatocin Jihohi su marawa kokarin da Gwamnatin Tarayya ke yi kan zuba nannun jari wajen samar da abinci, samar da kayan adana amfanin gona, tsarin rabar da amafnin gonar, kuma kamfanoni masu zaman kansu, musamman masu yin noma domin samun riba, suma suna da gudunmawr da za su bayar wajen kara bunkasa fannin aikin noma, musamman domina a tabbatar da cewa, abincin ya isa ga teburin, musamman marasa karfi, wadanda kuma za su rinka sayen abincin, a cikin farashi mai sauki.

Ya zama wajbi UNICEF, FAO, WEF, da sauran takwarororin su, da su kara kaimi wajen aikin sa kai a yankunan da karancin abinci ya fi kamari, domin taimakawa Gwamnati wajen wanzar da aikin na dogon zango.

A zaman mu na kasa, ba ta sabu mu yi ikirarin cewa, kasar na kan turba ba, bayan alhali, ‘yan kasar na ci gaba da fuskantar yunwa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciNigeria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Kara Sanya Harajin Fito Na Kaso 34% Kan Dukkan Kayayyakin Da Take Shigowa Daga Amurka

Next Post

2027: Tsananin Yunwa Zai Hana ‘Yan Nijeriya Sake Zaɓen Jam’iyyar APC – PDP

Related

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

3 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

5 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

6 hours ago
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi
Labarai

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

7 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

8 hours ago
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
Manyan Labarai

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

10 hours ago
Next Post
2027: Tsananin Yunwa Zai Hana ‘Yan Nijeriya Sake Zaɓen Jam’iyyar APC – PDP

2027: Tsananin Yunwa Zai Hana ‘Yan Nijeriya Sake Zaɓen Jam’iyyar APC – PDP

LABARAI MASU NASABA

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.