• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Yobe Sun Nuna Rashin Gamsuwarsu Kan Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar —Bincike

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Rahotonni
0
Jama’ar Yobe Sun Nuna Rashin Gamsuwarsu Kan Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar —Bincike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani sabon rahoto ya nuna yadda al’ummar jihar Yobe, dake Arewa Maso Gabashin Nijeriya suka nuna rashin gamsuwarsu da rashin sauke nauyin da ya hau wuyan kananan hukumomin jihar, tare da bukatar samun ingantuwar muhimman ayyukan raya yankunan karkara wanda ya rataya bisa wuyan kananan hukumomin.

Rahoton wanda aka yiwa taken: Rahoton Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar Yobe, ya saurari ra’ayoyin al’ummar jihar dangane da tabbatar da gamsuwa ko rashin gamsuwa da ayyukan kananan hukumomin.

  • Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

Sakamakon binciken, da aka fitar a ranar 18 ga watan Oktoba 2022, wanda kungiyar YMonitor ce ta gudanar dashi – wadda ke bibiya tare da tabbatar da ingantuwar tsarin Shugabanci da hadin gwiwa da kungiyar ‘The Future Project’ (TFP), wanda ya samu tallafin kungiyar ‘National Endowment for Democracy’.

A cikin takardar sanarwar da Shugaban dake jagorantar aikin YMonitor, Omidiji Olamilekan ya fitar yace, baya ga auna gamsuwar al’umma kan ayyukan kananan hukumominsu, rahoton har ila yau ya wayar da kan al’umma wajen sanin aikace-aikacen da suka rataya ga kananan hukumomin.

Bugu da kari kuma, binciken ya kunshi shawarwari ga hukumomi wajen farfado da tsarin kananan hukumomi a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Haka kuma, jwabin nasa ya zayyano sakamakon binciken wanda ya bayyana yadda al’umma suka nuna rashin gamsuwarsu da Shugabannin Kananan Hukumomi, inda sakamakon binciken ya gano yadda jama’ar ke nuna tsananin damuwa a kan harkokin siyasa da kuma sanin ayyukan kananan hukumomin a tsakanin al’ummar jihar Yobe.

Jagoran wannan binciken, Omidiji Olamilekan ya ce, “Wannan rahoton zai taimaki shugabannin kananan hukumomi wajen gano matsayin da suke, amfani da damar da suke da ita wajen daukar matakan da ya dace don cike gibin da ake dashi cikin hanzari tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.”

Har wala yau kuma, ta hanyar amfani da na’aurar bincike ta ‘Net Promoter Score Test’, sakamakon binciken ya bayyana yadda jama’ar jihar Yobe suka ki amincewa da nada Shugabannin kananan hukumomin jihar zuwa wasu manyan mukamai na gaba.

Inda a karshe binciken ya bayar da shawarar cewa akwai bukatar gwamnati ta shirya tarukan karawa juna sani ga Shugabannin Kananan Hukumomi domin samun kwarewar zamani da duniya ke amfani dashi yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NEMA Ta Karbi ‘Yan Nijeriya 137 Da Suka Makale A Kasar Libya 

Next Post

Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

15 hours ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

4 days ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

2 weeks ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 month ago
Next Post
Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.