• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Yobe Sun Nuna Rashin Gamsuwarsu Kan Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar —Bincike

by Muhammad Maitela
3 years ago
Yobe

A wani sabon rahoto ya nuna yadda al’ummar jihar Yobe, dake Arewa Maso Gabashin Nijeriya suka nuna rashin gamsuwarsu da rashin sauke nauyin da ya hau wuyan kananan hukumomin jihar, tare da bukatar samun ingantuwar muhimman ayyukan raya yankunan karkara wanda ya rataya bisa wuyan kananan hukumomin.

Rahoton wanda aka yiwa taken: Rahoton Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar Yobe, ya saurari ra’ayoyin al’ummar jihar dangane da tabbatar da gamsuwa ko rashin gamsuwa da ayyukan kananan hukumomin.

  • Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

Sakamakon binciken, da aka fitar a ranar 18 ga watan Oktoba 2022, wanda kungiyar YMonitor ce ta gudanar dashi – wadda ke bibiya tare da tabbatar da ingantuwar tsarin Shugabanci da hadin gwiwa da kungiyar ‘The Future Project’ (TFP), wanda ya samu tallafin kungiyar ‘National Endowment for Democracy’.

A cikin takardar sanarwar da Shugaban dake jagorantar aikin YMonitor, Omidiji Olamilekan ya fitar yace, baya ga auna gamsuwar al’umma kan ayyukan kananan hukumominsu, rahoton har ila yau ya wayar da kan al’umma wajen sanin aikace-aikacen da suka rataya ga kananan hukumomin.

Bugu da kari kuma, binciken ya kunshi shawarwari ga hukumomi wajen farfado da tsarin kananan hukumomi a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Haka kuma, jwabin nasa ya zayyano sakamakon binciken wanda ya bayyana yadda al’umma suka nuna rashin gamsuwarsu da Shugabannin Kananan Hukumomi, inda sakamakon binciken ya gano yadda jama’ar ke nuna tsananin damuwa a kan harkokin siyasa da kuma sanin ayyukan kananan hukumomin a tsakanin al’ummar jihar Yobe.

Jagoran wannan binciken, Omidiji Olamilekan ya ce, “Wannan rahoton zai taimaki shugabannin kananan hukumomi wajen gano matsayin da suke, amfani da damar da suke da ita wajen daukar matakan da ya dace don cike gibin da ake dashi cikin hanzari tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.”

Har wala yau kuma, ta hanyar amfani da na’aurar bincike ta ‘Net Promoter Score Test’, sakamakon binciken ya bayyana yadda jama’ar jihar Yobe suka ki amincewa da nada Shugabannin kananan hukumomin jihar zuwa wasu manyan mukamai na gaba.

Inda a karshe binciken ya bayar da shawarar cewa akwai bukatar gwamnati ta shirya tarukan karawa juna sani ga Shugabannin Kananan Hukumomi domin samun kwarewar zamani da duniya ke amfani dashi yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.